'An Rasa Rayuka': An Shiga Tashin Hankali a Neja da Nakiya Ta Tarwatse a Wani Gida

'An Rasa Rayuka': An Shiga Tashin Hankali a Neja da Nakiya Ta Tarwatse a Wani Gida

  • Wani abin fashewa ya tarwatse a wurin hakar ma’adanai a Sabon Pegi, karamar hukumar Mashegu, lamarin da ya jawo rasa rayuka
  • Rundunar ‘yan sanda ta ce fashewar na da alaƙa da tarwatsewar nakiya da aka ajiye a wani gidan zama don ayyukan hakar ma’adanai
  • Sarkin yankin, Muhammad Baiwa, ya yi kira da a kwantar da hankali tare da neman a ladabtar da masu ajiye nakiya a gidajensu

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Neja - Kwanaki kaɗan bayan fashewar tankar mai a Dikko, karamar hukumar Gurara, wacce ta halaka fiye da mutane 100, wata annobar ta sake afkuwa a Neja.

Tarwatsewar wani abin fashewa mai tsanani ya afku a wurin hakar ma’adanai a Sabon Pegi, karamar hukumar Mashegu, a safiyar Lahadi.

Mazauna Sabon Fegi sun yi magana da aka samu fashewar nakiya a garinsu
"Yan sanda sun fara farautar wanda ya zama silar fashewar nakiya da ta kashe mutane a Neja. Hoto: Big Bage
Asali: Facebook

Fashewar nakiya ta kashe mutane 6

Rahotannin farko sun nuna fashewar na da alaƙa da rashin kyakkyawan sarrafa kayan fashewa da ake amfani da su wajen hakar ma’adanai, inji rahoton Channels.

Kara karanta wannan

Sojoji su na ragargaza, an kai samamen dare a maboyar Boko haram

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wannan fashewa ta yi sanadiyyar mutuwar mutum hudu tare da raunata wasu da dama, kamar yadda mazauna garin Sabon Pegi suka shaida.

Shaidu sun ce fashewar ta girgiza yankin Sabon Pegi da kewaye, ciki har da New Bussa, inda jama’a suka tsere zuwa daji saboda tsoro.

Neja: 'Yan sanda sun fitar da rahoton farko

Sai dai, rundunar ‘yan sandan jihar Neja ta fitar da wata sanarwa daban, inda ta ce fashewar ta auku ne sakamakon ajiyar nakiya.

A cewar kakakin 'yan sandan, SP Wasiu Abiodun, nakiyar da wani Yushau ya ajiye a gidansa don ayyukan hakar ma’adanai ce ta fashe.

Wata mata mai suna Fatima Sadauki ta mutu, yayin da mutane shida suka ji raunuka, kuma suna karɓar magani a Asibitin Kainji, New Bussa.

Wanda ake zargi ya tsere bayan fashewar nakiyar

Fashewar ta lalata gidaje 12, kuma ana ci gaba da aikin ceto yayin da ake fargabar akwai wasu da suka makale a ƙarƙashin baraguzan gidaje.

Kara karanta wannan

Wata tankar man fetur ta sake fashewa a jihar Neja, ana fargabar mutane sun mutu

Rahotanni sun nuna cewa an ajiye nakiyar ne a wani gida kusa da wurin hakar ma’adanai, inda wannan wurin ya lalace gaba ɗaya.

Yushau wanda ake zargin shi ne ya jawo fashewar nakiyar, ya tsere kuma ba a san inda yake ba amma 'yan sanda sun ce suna ci gaba da bincike.

Sarkin yankin, Muhammad Baiwa, ya yi kira da a kwantar da hankali tare da ladabtar da masu ajiye nakiya a gidajen zamansu.

Bam ya tarwatse a makarantar Islamiyya

A wani labarin, mun ruwaito cewa dalibai biyu sun rasa rayukansu sakamakon fashewar wani abu a makarantar Islamiyya da ke ƙaramar hukumar Bwari, Abuja.

Wata majiya ta bayyana cewa ana zargin sabon ɗalibi ya kawo abin fashewar da ake tunanin bam ne, wanda ya jikkata ɗalibai da dama.

Ko da yake babu wata sanarwa daga ƴan sanda a hukumance, rahotanni sun nuna cewa jami'an tsaro sun isa makarantar kuma sun fara bincike kan lamarin.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.