Asiri Ya Tonu: Matasa Sun Yi Tara Tara, Sun Kama Malamai 2 da Wasu Abubuwan Ban Mamaki

Asiri Ya Tonu: Matasa Sun Yi Tara Tara, Sun Kama Malamai 2 da Wasu Abubuwan Ban Mamaki

  • Matasa sun cafke wasu malaman coci a jihar Ribas bisa zarginsu da aikata wasu baƙin abubuwa, an gano kayayyakin ban mamaki a cocinsu
  • Rundunar ƴan sanda ta bayyana cewa a binciken farko, ta gano alburushi mai rai, takobi da wasu akwatuna na itace
  • Ɗaya daga cikin limaman cocin da suka shiga hannu, ya ce ya jima yana taimakon al'umma a yankin

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Rivers - Matasa sun ritsa wasu limamai biyu, sun kama su a jihar Ribas saboda gano alburushi da kayayyaki a majami'un da suke wa'azi.

Waɗanda ake zargin, Fasto Umoren Bassey da Fasto Elijah Aniete, sun shiga hannu ne ranar 20 ga Janairu, 2025, a kauyen Rumunduru da ke karamar hukumar Obio/Akpor.

Yan sanda.
An kama malaman coci 2 da alburushi da wasu kayan ban mamaki a Ribas Hoto: @PoliceNG
Asali: Twitter

Bayan kama su, matasan ba su yi wata-wata ba suka miƙa su ga rundunar ƴan sanda, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga 30 sun shiga har cikin daki sun sace mata da miji a Abuja

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An tattaro cewa malaman cocin ba su wuce shekaru 60 da 51 ba a duniya kuma dukkansu ƴan asalin jihar Akwa Ibom ne.

Yan sanda sun tabbatar da cafke malamai 2

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Grace Iringe-Koko, ta gabatar da wadanda ake zargin a hedkwatar ‘yan sanda da ke Fatakwal ranar Alhamis.

Ta bayyana cewa a binciken farko an gano abubuwa masu ban mamaki a cikin cocin da fastocin ke jagoranta.

Abubuwan da aka gano sun hada da harsashi mai rai, takobi, akwatuna biyu na itace, fasfon sufurin ruwa na jabu, hotuna da fasfon dubban mutane.

Abubuwan da aka gano a cocin limaman

Sauran abubuwan da aka gano a cocin sun hada da kwalabe dauke da sindarin da ba sani ba, takalman yara, akwatunan bokanci, kwakwa, littattafan Biyibul, kayan ‘yan sanda, da sauran kayan tsafi daban-daban.

Sai dai, babu maciji ko babban akwatin gawa kamar yadda rahotannin farko suka yi ikirari.

Kara karanta wannan

Hankula sun tashi bayan 'yan bindiga sun kashe farfesan jami'a a gidansa

Kakakin ƴan sandan ta ce cocin Fasto Bassey mai suna God Deliverance Apostolic Church da ta Fasto Aniete mai suna Power House of Glory International Church suna kan titin Eneka a Rumunduru a karamar hukumar Obio-Akpor.

Fasto ya faɗi dalilin tara kayan a coci

Da yake jawabi, ɗaya daga cikin malaman cocin da aka cafke, Fasto Bassey ya ce yana amfani da kayan tsafi wajen yin addu’a kamar yadda Allah ya umarce shi.

Sai dai ya yi zargin cewa al’ummar yankin ne suka ƙulla masa makirci suka sanya wasu daga cikin kayan da aka gano a cocinsa sannan suka bincike gidansa ba tare da izini ba.

“Na dade ina warkar da mutane daga rashin lafiya kuma ina taimakon al’umma. Na yi shekaru 17 ina zama a wurin. Wasu daga cikin hotunan da kuka gani na da ne.
"Ina amfani da karamin akwatin gawa ko man al’ajabi wajen yi wa masu tabin hankali addu’a, duk mahaukacin da aka kawo mani yana samun nutsuwa cikin watanni uku, ina haka ne don taimakon mutane."

Kara karanta wannan

Maganar N Power ta dawo, Tinubu ya umarci sake fasalinta, matasa za su caɓa

Wasu ƴan fashi sun shiga hannu

Kun ji cewa yan sanda sun yi nasarar cafke wasu mutum uku da ake zargi da aikata laifin fashi da makami a jihar Kano.

Ƴan sanda sun gano kayayyaki a hannun ƴan fashin wada suka haɗa da wuƙaƙe da wayar salula, za a gurfanar da su a kotu bayan gama bincike.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262