Bauchi: Gidauniya Ta Raba Littattafai Miliyan 1 Saboda Inganta Ilimi, an Yaba Mata

Bauchi: Gidauniya Ta Raba Littattafai Miliyan 1 Saboda Inganta Ilimi, an Yaba Mata

  • Gidauniyar Ibrahim Ali Usman ta tallafawa ɗalibai da littattafai domin inganta harkokin ilimi a jihar Bauchi da ke Arewacin Najeriya
  • Gidauniyar ta ƙaddamar da tallafin litattafai akalla 1,050,000 domin tallafa wa ɗaliban Bauchi ta Kudu a wani babban taro
  • Shugaban Gidauniyar, Hon. Ibrahim Ali Usman ya bayyana cewa 'Ibrahim Ali Usman Foundation' za ta cigaba da tallafawa ilimi a jihar musamman mata da yara
  • Kungiyoyi da dama sun karrama Hon. Ibrahim Ali Usman bisa gudunmawar da yake bayarwa kamar yadda mai magana da yawun Gidauniyar ya fadawa Legit Hausa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Bauchi - Wata Gidauniya a jihar Bauchi ta ba da tallafin littattafai ga ɗalibai a yankin Bauchi ta Kudu da ke Arewacin Najeriya.

Shugaban Gidauniyar, Hon. Ibrahim Ali Usman ya ƙaddamar da tallafin litattafai guda 1,050,000 ga ɗaliban domin inganta harkokin ilmi.

Kara karanta wannan

Kano: Abba Gida Gida ya jawo hadimin Kwankwaso, ya nada shi a Mukami

Gidauniya ta raba littattafai 1m ga ɗalibai a Bauchi
Gidauniyar Alhaji Ibrahim Usman Bauchi ta yi rabon littattafai 1m ga ɗalibai a Bauchi. Hoto: No Shaking.
Asali: Facebook

Gidauniya ta warkar da makafi a Kano

Daraktan yada labaran Gidauniyar, Nuruddeen Yakubu Haske shi ya tabbatar da haka ga wakilin Legit Hausa a yau Alhamis 16 ga watan Janairun 2025.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gidauniyoyi da dama na taimakon al'umma a bangarori da yawa domin inganta rayuwar mutane da kuma marasa karfi.

A baya, mutane akalla 3,000 suka ci gajiyar Gidauniyar dan Majalisar Tarayya a jihar Kano, Hon. Umar Datti bayan yi musu tiyata kyauta.

Gidauniyar ta taimaki makafi da dama inda ta yi musu aiki kyauta tare da yin nasarar dawo musu da idanunsu.

Gidauniyar karkashin shugabancin Hon. Yusuf Umar Datti ta yi nasarar yi wa mutane 3,000 tiyatar ido ba tare da sun biya ko sisin kwabo ba.

Wadanda suka ci gajiyar sun fito ne daga mazabar dan Majalisar Tarayya, Hon. Datti Kura ta Kura/Garunmallam/Madobi da ke jihar Kano.

Gidauniyar Ibrahim Usman ta tallafa wa dalibai

Kara karanta wannan

Ganduje ya sabunta katafaren masallaci, malamai da 'yan siyasa sun hallara

Yakubu Haske ya fadawa Legit Hausa cewa Gidauniyar tana da niyyar ci gaba da tallafawa ilimi musamman a kananan hukumomin Bauchi ta Kudu.

Ya ce kowace karamar hukuma daga cikin bakwai a Bauchi ta Kudu za ta samu litattafai 150,000 domin ilmantar da yara da inganta rayuwar matasa.

Gidauniya ta raba wa dalibai littattafai a Bauchi

An karrama shugaban Gidauniyar, Hon. Ibrahim Usman

Haka kuma, ya jaddada cewa gidauniyar za ta ci gaba da ayyukan alheri musamman ga mata da yara domin cigaban al'umma.

Daga bisani, ya ce kungiyoyi daban-daban sun karrama Alhaji Ibrahim Ali Usman bisa jajircewarsa a taimakon al'umma, musamman a Bauchi ta Kudu.

Shugaban Gidauniyar, Ibrahim Ali Usman ya roki Allah SWT ya bashi ƙarfi da hikima domin cigaba da ayyukan alheri da ci gaban jihar Bauchi.

An gudanar da addu'o'i ga Gwamna Kefas

A wani labarin, al'ummar Musulmi sun gudanar da addu'o'i na musamman ga Gwamna Agbu Kefas na jihar Taraba.

Kara karanta wannan

Abin da Kashim Shettima ya ce kan bikin Maulidi a Kano duk da zargin kokarin hana taron

An gudanar da addu'o'in ne a ranar Asabar 4 ga Janairun 2025 domin Gwamna Kefas da kuma ci gaban jihar Taraba gaba daya.

Hadimin gwamnan a bangaren harkokin addinin Musulunci ya ce sun taru a masallacin Juma'a na Saurara ne da ke birnin Jalingo domin addu'o'in zaman lafiya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.