Matar Tinubu Ta Raba Miliyoyi a Arewacin Najeriya, Za a yi Rabo a Dukkan Jihohi
- Matar shugaban kasa, Oluremi Tinubu ta raba miliyoyin kudi ga mata a jihar Zamfara domin bunkasa ƙananan sana'o'i
- An ruwaito cewa mata 1,000 ne suka samu kyautar tallafin a wannan karon yayin da matar shugaban kasar ta samu wakilci
- Matar shugaban kasar ta tabbatar da cewa za ta zagaya dukkan jihohin Najeriya domin raba kudin ga mata masu sana'a
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Jihar Zamfara - Matar mai girma shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ta ba mata tallafin kudi a jihar Zamfara.
An ruwaito cewa Oluremi Tinubu ta raba zunzurutun kudi har N50m ga mata domin bunkasa kananan sana'o'i.

Asali: Twitter
Jaridar Daily Trust ta wallafa cewa matar gwamnan jihar Zamfara ce ta wakilci Oluremi Tinubu yayin rabon kudin.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Matar Tinubu ta raba N50m a Zamfara
Matar shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ta raba kudi N50,000 ga mata domin bunkasa sana'a a jihar Zamfara.
Tribune ta wallafa cewa mata guda 1,000 ne suka samu kyautar kuma kowace daya ta samu N50,000 daga cikin N50m.
Dalilin rabawa mata miliyoyi a Zamfara
Matar gwamnan jihar Zamfara, Hajiya Hurriya Dauda Lawal ta ce an raba kudin ne domin a tallafi mata masu kananan sana'o'i.
Hajiya Hurriya ta ce ƙananan sana'o'i ne kashin bayan tattalin arziki saboda haka tallafa musu zai taimaka wa tattali.
Matar Tinubu za ta yi rabo a sauran jihohi
Matar shugaban kasar ta bayyana cewa tallafin kudin na cikin kokarin da gwamnatin Tinubu take yi kuma za a zagaya dukkan jihohin Najeriya.
Oluremi Tinubu ta bayyana cewa a zuwa yanzu mata 70,000 ne suka ci moriyar shirin a fadin Najeriya.
An kaddamar da ba mata tallafi a Borno
A wani rahoton, kun ji cewa matar shugaban kasar Najeriya, Sanata Oluremi Bola Ahmed Tinubu, ta kaddamar da shirin ba da tallafi ga mata a jihar Borno.
Uwargidar Najeriyar ta samu wakilcin matar mataimakin shugaban kasa, Hajiya Nana Kashim Shettima yayin kaddamar da shirin a birnin Maiduguri.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng