'Yan Bindiga Sun Jefa Bama Bamai a Hedkwatar Ƴan Sanda, Sun Tafka Ta'asa
- Jami'i ɗaya ya mutu da ƴan bindiga suka kai mummunan farmaki a hedkwatar ƴan sanda da ke garin Oba a jihar Anambra
- Mai magana da yawun ƴan sandan jihar, Tochukwu Ikenga ya ce maharan sun riƙa jefa bama-baman kwalabe a wannan harin
- Ya ce tuni jami'an tsaro da suka haɗa da sojoji, ƴan sanda da sauran dakarun hukumomin tsaro suka fara farautar maharan
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Anambra - Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan aware ne sun kai hari hedikwatar ‘yan sanda da ke garin Oba karamar hukumar Idemili ta Kudu a Anambra.
Rahotannin da muka samu sun nuna cewa ƴan ta'addan sun kashe kofur na ƴan sanda a harin wanda suka kai da safiyar ranar Talata, 3 ga watan Satumba, 2024.

Asali: Facebook
Mahara sun yi wa ƴan sanda ta'asa
Wata majiya ta shaidawa Daily Trust cewa maharan sun kashe kofur tare da jikkata wasu jami'an ƴan sanda da ke aiki a hedikwatar.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Majiyar ta ƙara da cewa ‘yan bindigar sun kuma kai hari a cibiyar Oba Civic Centre, har yanzu babu cikakken bayani kan dalilin kai wannan hari.
Amma harin ya zo a daidai lokacin da jagoron ƴan aware, Simon Ekpa, ya yi barazanar sa ƙafar wando ɗaya da duk wani abu da ya shafi gwamnati a Kudu Maso Gabas.
Ƴan sanda sun faɗi matakin da aka ɗauka
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda jihar Anambra, SP Tochukwu Ikenga, ya tabbatar da kai harin a wata sanarwa da ya fitar.
Ya ce tuni dakarun haɗin guiwa da suka kunshi, sojoji, jami'an tsaron fararen hula NSCDC da sauran hukumomin tsaro suka fara farautar maharan a Oba da Kewaye.
Kakakin ƴan sandan ya ce maharan sun buɗe wuta kan mai uwa da wabi da kuma jefa bama-baman kwalaben fetur a hedkwatar ƴan sandan, Punch ta kawo labarin.
"Abin takaicin kofur ɗaya wanda ya ji munanan raunuka a harin ya rasa ransa daga baya amma an yi nasarar kashe wutar da ta tashi da taimakon jami'an tsaro," in ji Ikenga.
Ƴan bindiga sun kai farmaki sakatariya a Anambra
A wani rahoton kun ji cewa wasu yan bindiga kimanin 30 sun dura ƙaramar hukumar Ogbaru a jihar Anambra inda suka bude wuta a sakatariya.
Rahotanni sun nuna cewa yan bindigar sun yi kone kone a karamar hukumar kafin su yi musayar wuta da yan sandan jihar.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng