Wani Abin Fashewa da Ake Zargin 'Bam' Ne Ya Tarwatse a Fitacciyar Kasuwa a Arewa
- Wani abun fashewa da ake kyautata zaton bam ne ya tashi a kasuwar shanu da ke garin Buni Yadi a ƙaramar hukumar Gujba ta jihar Yobe
- Rahotanni sun bayyana cewa bayan tashin bam ɗin, sojoji sun sake gano wani bam da aka dasa a kasuwar amma sun kwance shi
- Lamarin ya faru ne da tsakar rana yau Jumu'a kuma ya raunata wata yarinya, yanzu haka tana kwance a asibiti ana kula da lafiyarta
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jihar Yobe - Wani abin fashewa da ake kyautata zaton 'bam' ne ya tarwatse a babbar kasuwar Buni Yadi da ke karamar hukumar Gujba a jihar Yobe.
Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 12.30 na tsakar rana yau Jumu'a, 26 ga watan Yuli, 2024.

Asali: Original
Wani mazaunin garin Buni Yadi, Ali Alhassan ya shaidawa gidan talabijin na Channels ta wayar tarho cewa tashin bam ɗin ya jikkata wata yarinya.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Sojoji sun kwance bam a Yobe
Kakakin rundunar hadin gwiwa ta sashe na 2 na Operation Hadin Kai, Kyaftin Muhammad Shehu shi ma ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce sojoji sun sake gano wani ƙarin bam da aka dasa a kasuwar kuma sun yi nasarar kwance shi, kamar yadda Leadership ta tattaro.
Ya kara da cewa a halin yanzu mutum daya da lamarin ya rutsa da shi yana kwance yana karbar magani a daya daga cikin asibitocin da ke Buni Yadi.
Kyaftin Muhammad Shehu ya yi ƙarin haske da cewa lamarin ya auku ne sakamakon dasa bam da aka yi a kasuwar ba wai harin ƙunar bakin wake ba ne.
Tashin bam ya lafa a jihar Yobe
Legit Hausa ta tattaro cewa Buni Yadi na da tazarar kilomita 54 daga Damaturu babban birnin jihar Yobe a yankin Arewa maso Gabas.
Ita ce karamar hukumar da ta fi fama da hare-hare a jihar Yobe lokacin da mayakan Boko Haram suka ci karensu ba babbaka tsawon shekaru biyu.
Ƴan fashi sun baƙunci lahira a Abuja
A wani rahoton kuma yan sanda sun hallaka ƴan fashi biyu bayan sun kwato motar Jeep a babban birnin tarayya Abuja a daren ranar Alhamis.
Kwamishinan ƴan sandan babban birnin tarayya, CP Benneth Igweh ya ce sun kama ragowar ƴan fashin bayan musayar wuta.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng