Jira Ya Ƙare, Shugaba Tinubu Zai Sanar da Adadin Sabon Mafi Ƙarancin Albashi a Najeriya
- Mai yiwuwa shugaban ƙasa, Bola Ahned Tinubu ya sanar da sabon mafi ƙarancin albashin ma'aikata yau Alhamais, 18 ga watan Yuli
- Wannan na zuwa ne bayan Bola Tinubu ya buƙaci majalisa ta ƙara makudan kudi a kasafin kuɗin 2024 saboda ƙarin albashin da za a yi
- Ana sa ran duk wani jira ya ƙare, Tinubu na iya bayyana adadin bayan ganawa da ƴan kwadago a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
FCT Abuja - Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu na iya sanar da adadin sabon mafi ƙarancin albashin ma'aikata a Najeriya yau Alhamis, 18 ga watan Yuli, 2024.
Ana tsammanin za a bayyana sabon albashin ne a lokacin da shugaba Tinubu da ƴan kwadago suka koma teburin tattaunawa a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Asali: Twitter
Rahoton Independent ya nuna cewa a taron da suka yi na ƙarshe, Bola Tinubu ya ce ba dole sai an jira bayan shekaru biyar kafin a sake duba mafi ƙarancin albashi ba.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A cewarsa, ya kamata a ce duk bayan shekara biyu zuwa uku a sake komawa teburin tattaunawa kan albashin ma'aikatan ƙasar nan.
Tinubu ya buƙaci ƙarin N6.2trn a kasafin 2024
Ranar Laraba, 17 ga watan Yuli, 2024, Bola Tinubu ya buƙaci majalisar dattawa ta ƙara N6.2trn a kasafin kuɗin 2024.
Shugaban masu rinjaye na majalisar, Sanata Opeyemi Bamidele (APC, Ekiti ta Tsakiya), ya ce kara kuɗin kasafin ya zama dole saboda saboda mafi ƙarancin albashi.
A lokacin da yake gabatar da kudirin jiya Laraba, Sanata Bamidele ya ce bayan ƙarin albashi, za a yi amfani da kudin wajen yin wasu ayyuka da tun farko ba a sa su a kasafin ba.

Kara karanta wannan
Gwamnonin PDP sun goyi bayan NLC, sun faɗi matsaya kan sabon mafi ƙarancin albashi
Bugu da ƙari, ana sa ran yau Bola Tinubu da wakilan ƙungiyoyin kwadago za su ƙarƙare batun ƙarin albashin a taron da aka tsara gudanarwa a Villa, Punch ta ruwaito.
Gwamnonin PDP sun faɗi matsayarsu
Kuna da labarin Gwamnonin jam'iyyar PDP sun bayyana goyon bayan buƙatar NLC na ƙarin mafi ƙarancin albashin ma'aikata a Najeriya.
A wata sanarwa da kungiyar gwamnonin ta fitar bayan taro a Enugu, ta buƙaci a yi la'akari da ƙarfin arzikin gwamnatoci kafin yanke adadin ƙarin.
Asali: Legit.ng