Gwamnan Adamawa Ya Yiwa Gwamnatinsa Garambawul, an Sauya Wasu Kwamishinoni

Gwamnan Adamawa Ya Yiwa Gwamnatinsa Garambawul, an Sauya Wasu Kwamishinoni

  • An samu sababbin sauye-sauye a majalisar kwamishinonin jihar Adamawa bayan Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri ya yi wani garambawul
  • Sauyin da gwamnan ya yi ya shafi wasu ma'aikatu guda huɗu ne waɗanda aka bayyana kwamishinonin da za su ci gaba da jan ragamarsu
  • Gwamnan ya ce ya yi hakan ne da nufin ƙara ƙarfin gwiwar kwamishinonin domin inganta ayyukan da suke yiwa mutanen jihar

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Adamawa - Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri a ranar Litinin ya yiwa majalisar kwamishinoninsa garambawul.

Gwamnan ya yi hakan ne da nufin ƙara ƙarfin gwiwar kwamishinonin domin inganta ayyukan da suke yiwa al'ummar jihar.

Fintiri ya yi garambawul a gwamnatinsa
Gwamna Fintiri ya sauyawa wasu kwamishinoni ma'aikatu a Adamawa Hoto: Ahmadu Umaru Fintiri
Asali: Facebook

Da yake sanar da yiwa majalisar kwaskwarima a ranar Litinin a Yola, babban sakataren yaɗa labarai na gwamnan, Mista Humwashi Wonosikou, ya ce sauye-sauyen sun shafi ma'aikatu huɗu ne nan take, cewar rahoton jaridar Leadership.

Kara karanta wannan

Gwamna ya kori kwamishinan ayyuka na musamman daga aiki, ya tura masa saƙo

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Fintiri ya yi garambawul a Adamawa

Humwashi Wonosikou ya bayyana cewa a yanzu an mayar da tsohuwar kwamishinar yaɗa labarai, Neido Geoffrey Kufulto muƙamin kwamishinan harkokin mata, rahoton Daily Post ya tabbatar.

Tsohon kwamishinan kasuwanci, James Iliya ya koma muƙamin kwamishinan yaɗa labarai.

Yanzu Mista Hamajumba Gatugel ya zama kwamishinan harkokin kasuwanci yayin da Misis Wunfe Anthony ta zama kwamishiniyar sufuri.

Gwamnan Adamawa a kan kwamishinoninsa

Gwamna Fintiri ya bayyana ƙwarin gwiwar cewa kwamishinonin za su iya sauke nauyin da aka ɗora musu.

Gwamnan ya yi gargaɗi game da yin zagon ƙasa, ya kuma buƙaci kwamishinonin da su yi aikinsu yadda ya kamata.

Fintiri ya kuma buƙaci kwamishinonin da abin ya shafa da su yi aiki tare domin an miƙa mulki yadda ya kamata ba tare da samun wata tangarɗa ba.

Gwamna Fintiri ya yi naɗi a Adamawa

Kara karanta wannan

'Yan ƙwadago na shirin ɗaukar mataki bayan Gwamnatin Tinubu ta miƙa tayin N62,000

A wani labarin kuma, kun ji cewa Gwamna Ahmadu Fintiri na Adamawa ya amince da nadin Mustapha Amin, Galadiman Adamawa, a matsayin Amirul Hajj na aikin Hajjin 2024.

Babban sakataren yaɗa labaran gwamnan, Humwashi Wonosikou, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a birnin Yola, babban birnin jihar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng