Kwararren Mai Kerawa Boko Haram Bama Bamai Ya Mika Wuya a Borno

Kwararren Mai Kerawa Boko Haram Bama Bamai Ya Mika Wuya a Borno

  • Shahararren mai kera wa 'yan kungiyar Boko Haram bama-bamai ya mika wuya ga jami'an tsaro a jihar Borno
  • Kakakin rundunar hadin kai mai yaki da ta'addanci a jihar Borno, Laftanal Kanal Abubakar Abdullahi ne ya bada sanarwar
  • Ya kuma yi kira ga sauran 'yan ta'addan da ke boye cikin dazuka da su fito su mika wuya ga jami'an tsaro

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Kwararren mai kerawa kungiyar ta'addanci ta Boko Haram bama-bamai tare da wani dan kungiyar guda daya sun mika wuya ga jami'an tsaro a jihar Borno.

Nigerian Army
Sojin Najeriya sun yi kira ga 'yan ta'adda su rika mika wuya. Hoto: HQ Nigerian Army
Asali: Twitter

Mutanen sun mika wuya ne ga jami'an sashen na uku na rundunar haɗin guiwa mai yaki da ta'addanci da ke Munguno a jihar Borno.

Kara karanta wannan

Sojoji sun gano gidan burodin 'yan ta'addan ISWAP a jihar Borno

Jaridar Leadership ta ruwaito cewa sun mika wuyan ne ranar Lahadi, 21 ga watan Afrilu bayan an umurcesu da su kai hari.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

'Yan ta'addan da suka mika wuya

Sanarwar da kakakin rundunar, Laftanal Kanal Abubakar Abdullahi, ya bayar ta nuna cewa mai hada bama-baman ya ce sunansa Abubakar Muhammad (Garba) kuma shekarunsa 19 ne.

Daya dan ta'addan da suka mika wuya tare kuwa sunansa Bana Modu mai shekaru 13 da haihuwa, a cewar jaridar Premium Times

Kakakin ya kara da cewa lokacin da ake bincikensu sun tabbatar da cewa an umarce su ne da su dasa bama-bamai a titunan garin Baga da ke karamar hukumar Kukawa a jihar Borno.

Amma a cewarsu, sai suka mika wuya ga jami'an tsaro domin su nuna tuba daga aikin ta'addanci da suka saba yi.

Boko Haram: Jawabin rundunar soji

Kara karanta wannan

Abin da ba a taba yi ba: Dan Najeriya ya kafa tarihi a duniyar wasan 'Chess', Tinubu ya yaba masa

A cewar kakakin rundunar, mika wuyan ya nuna kokarin da rundunar hadin kai a kan yaki da ta'addanci take yi a kan samar da zaman lafiya yana haifar da da mai ido.

Kuma hakan kamar kira ne ga sauran 'yan ta'addan da suke yankin a kan su fito su mika wuya ga jami'an tsaro domin samar da zaman lafiya mai dorewa a jihar.

An kashe 'yan Boko Haram a Borno

A wani rahoton kuma, kun ji cewa dakarun sojoji sun samu nasarar yin galaba kan ƴan ta'adda a dajin Sambisa da ke jihar Borno ta yankin Arewa maso gabashin Najeriya.

A wani farmaki da sojojin suka kai cikin dajin sun sheƙe ƴan ta'adda uku tare da lalata maɓoyarsu da suke amfani wajen ɓoyewa

Asali: Legit.ng

Online view pixel