Shehu Sani Ya Yi Martani Bayan Shugaba Tinubu Ya Samu Babban Mukami a Afirika

Shehu Sani Ya Yi Martani Bayan Shugaba Tinubu Ya Samu Babban Mukami a Afirika

  • Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani ya mayar da martani kan sabon muƙamin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya samu
  • A ranar Juma'a, Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU ) ta naɗa Shugaba Tinubu a matsayin zakaran samar da lafiya a Afirika
  • Sani ya ce bayan da Super Eagles ta Najeriya ta yi rashin nasara a wasan ƙarshe na AFCON a hannun Ivory Coast, yanzu ƙasar ta zama zakaran lafiya a Afirika

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Tsohon Sanatan Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani ya bayyana sabon matsayin Najeriya a nahiyar Afirika.

Sani ya ce Najeriya yanzu ta zama zakaran lafiya a Afirika bayan Super Eagles ta yi rashin nasara a gasar cin kofin AFCON 2023 a hannun mai masaukin baki, Ivory Coast a ranar Lahadi, 11 ga watan Fabrairu.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu zai gana da gwamnonin Najeriya kan muhimmin abu, bayanai sun fito

Shehu Sani ya magantu kan sabon mukamin Tinubu
Shehu Sani ya ce Najeriya ta samu sabon mukami bayan rasa kofin AFCON Hoto: Shehu Sani, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

Ya bayyana hakan ne a shafinsa na X (wanda a baya aka fi sani da Twitter) @ShehuSani, a ranar Juma’a, 16 ga watan Fabrairu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake mayar da martani ga muƙamin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya samu a ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU).

A kalamansa:

"Mun yi rashin nasara a gasar AFCON a Abidjan amma yanzu mun zama 'Zakarun lafiya' a Afirika."

Ƴan Najeriya sun mayar da martani yayin da Tinubu ya samu sabon muƙami

ŘÊ£ΊŤ@simpleiykejnr

"Lafiya a Afirka! Shugabanmu da ƴan siyasarmu har yanzu suna fita waje don neman lafiya…"

Adams @osagie_adams

"Kar a yi ƙarya, tun da Bulaba yana zuwa Faransa a kodayaushe don duba lafiyarsa, mun cancanci zama a cikin matsayi na ɗaya akan lafiya."

clinton @esiabaclinton1

"Zakaran lafiya yana zuwa Faransa don samun kulawar likitoci. Kun cika wasa a ƙasar nan."

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya naɗa mutum 5 a manyan muƙamai a babban banki CBN, ya tura saƙo Majalisa

Evergreen @Chris_Okp

"Ɓabu abin da Allah ba zai iya yi ba."

Easy@TadeOmole

Balablue din mu har yanzu yana tafiya a duba lafiyarsa a ƙasar waje, har ma za ka iya samun sirinji a asibitin Aso Villa. Zakaran bala'i.

Afenifere Sun Goyi Bayan Tinubu

A wani labarin kuma, kun ji cewa ƙungiyar Yarabawa ta Afenifere ta caccaki masu sukar gwamnatin Tinubu kan halin matsin tattalin arziƙin da ake ciki a ƙasar nan.

Ƙungiyar ta bayyana cewa masu sukar Tinubu sun yi shiru a lokacin mulkin Buhari wanda shi ne ya jawo halin da ake ciki a ƙasar nan.

Asali: Legit.ng

Online view pixel