“Abun Dariya”: Kotu Ta Nemi Yaron da Aka Zarga da Satar Keke Ya Biya N2m Kudin Beli

“Abun Dariya”: Kotu Ta Nemi Yaron da Aka Zarga da Satar Keke Ya Biya N2m Kudin Beli

  • Wata kotun majistare da ke Ogba, Ikeja a jihar Lagas ta bayar da belin wani yaro da aka zarga da satar keke kan kudi naira miliyan 2
  • Wani lauyan Najeriya, Olanipekun Tobi, ya koka a shafinsa na X (wanda aka fi sani da Twitter a baya) a ranar Juma'a
  • A cewar Olanipekun, irin wannan hukunci shine dalilin da yasa gidan yara halin Najeriya ya cika da jama'a

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

Ikeja, jihar Lagos - Wani lauyan Najeriya mai suna Olanipekun Tobi, ya koka bayan wata kotun majistare da ke Ogba, Ikeja a jihar Lagas ta bayar da belin wani yaro da aka zarga da satar keke kan kudi naira miliyan 2.

Kara karanta wannan

Ni na fatattaki Shekau da Qaqa, da yanzu Niger ta zama hedikwatar Boko Haram, tsogon gwamna Aliyu

Olanipekun ya ce wannan ne dalilin da yasa gidan gyara hali ya cika da jama'a a Najeriya.

Kotu ta ba da belin barawon keke kan miliyan 2
“Abun Dariya”: Kotu Ta Nemi Yaron da Aka Zarga da Satar Keke Ya Biya N2m Kudin Beli Hoto: Court of Appeal
Asali: UGC

Ya kara da cewar farashin keken da aka zargi yaron da sacewa bai kai N50,000 ba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Lauyan ya bayyana hakan ne ta shafinsa na X (wanda aka fi sani da Twitter a baya) @OlanipekunTobiD, a ranar Juma'a, 1 ga watan Disamba.

Ya rubuta:

"Akwai wata kotun majistare a Ogba, wacce ta kafa sharudan belin wani yaro da aka zarga da sace babur. Ku cinka sharudan?
"Naira miliyan 2!
"Belin naira miliyan boyu ga yaron da aka zarga da satar kek wanda bai ma kai ko 50k ba.
"Sannan kuna mamakin yadda aka yi kurkukunmu suka cika da mutane."

Yan Najeriya sun yi martani

Da yake martani ga sharadin belin alkalin kotun, fitaccen lauya, Inibehe Effiong, ya bayyana hakan a matsayin abin ban haushi da ban dariya!

Kara karanta wannan

Bani da katabus: Wanda ya kone takardar digirinsa ya yi bayanin dalilansa na bankawa takardunsa wuta

@InibeheEffiong:

"Abun ban haushi da dariya"

@Brown__Sophie:

"Abun haushi.

"Sannan za ku fada mani cewa alkalin kotun majistaren zai iya bacci da kyau da daddare."

@masurge7:

"Ina mamakin idan wadannan mutanen da ke kan benci mutane ne."

@EbunoluwaD_ :

"Wow
"Ta ina har suka zo da abubuwa irin wannan?
"Wannan wane irin abin ban dariya ne?"

Matashi ya yi girki mai tsada

A wani labari na daban, wani dan TikTok ya yi kokarin shirya abinci, amma sai ya kare da soya wayarsa kirar iPhone a maimakon haka. Ya yada yadda al'amarin ya faru a TikTok, inda abun ya yadu.

An san wayoyin iphone da shegen tsada, kama daga R6k zuwa sama da R30k, saboda haka kona daya an jikin tukunya ba karamin al'amari bane.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng