“Duk Namijin da Ya Aureni Ya Taki Sa’a”: Budurwa Mai Hannu Daya Ta Yaba Surar Da Allah Ya Yi Mata

“Duk Namijin da Ya Aureni Ya Taki Sa’a”: Budurwa Mai Hannu Daya Ta Yaba Surar Da Allah Ya Yi Mata

  • An gano wata matashiyar budurwa wacce ke da hannu daya tana rawa tare da baje koli surar jikinta a bidiyon TikTok da ya yadu
  • Matashiyar ta ce komai ya ji a jikinta sannan ta bugi kirjin cewa duk mutumin da ya aureta ya taki sa'a
  • Bidiyon ya yi fice a TikTok yayin da mutane da dama suka amince da ikirarin budurwar sannan suka jinjina kyawunta a sashin sharhi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

Wata kyakkyawar budurwa wacce ke da hannu daya ta yada wani bidiyo a TikTok inda ta ce komai ya ji a jikinta.

A cikin bidiyon, matashiyar mai suna Maryann Officiall, ta zage tana kwasar rawa a cikin wani daki tana mai baje kolin dirarren surar jikinta mai matukar kyau.

Kara karanta wannan

"204k kullun, N6.1m duk wata": Dan Najeriya da ke jinyar wani tsoho ya bayyana abun da yake samu

Maryann ta ce duk wand aya aure ta ya yi sa'a
“Duk Namijin da Ya Aureni Ya Taki Sa’a”: Budurwa Mai Hannu Daya Ta Yaba Surar Da Allah Ya Yi Mata Hoto: TikTok/@maryann_officiall.
Asali: TikTok

Ta bayyana karara cewa duk mutumin da ya aureta yana da matukar sa'a a rayuwa saboda mutumin ya samu kyakkyawar mace.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Duk da kasancewarta mai bukata ta musamman, Maryann na iya bakin kokarinta don ganin ta kasance cikin farin ciki a rayuwa.

Shafinta na TikTok na kunshe da tarin bidiyoyi da ke nuno ta tana rawa da baje kolin kyawunta.

Ta yi wa sabon bidiyon take da:

"Mijina na da sa'a ba kadan ba, kalli cikakken kaya mana. Kana zolayata ne."

Kalli bidiyon a kasa:

Jama'a sun yi martani kan bidiyon kyakkyawar mata mai hannu daya

@Janice B ta ce:

"Shin wai har mutane sun manta halin da matar nan ta shiga ne? Ko dai sabbin zuwa ne ke yin martani mara dadi? Ina zuciyarku na tausayi?"

@Shamaunbeatable ta ce:

Kara karanta wannan

Kano: Takardar CTC ta nuna Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da nasarar Gwamna Yusuf, Femi Falana

"Wasu mutane basu da hankali da tausayi. Dubi irin martanin da suke ajiyewa. Allah ya kyauta."

@user6168777203075 ya ce:

"Ci gaba da gashi. Wasu da suke da hannu basu cimma abun da kika cimma ba. Don Allah kada ki kula wadannan martanin marasa dadi."

@mofieyisetanire ta ce:

"Ba a yi wa wasu horo da soyayya ba, ina mamakin wasu mutane za su iya rubuta irin wannan martanin."

Makudan kudaden da dan agaji ke samu

A wani labarin, mun ji cewa wani dan Najeriya da ke zaune a Birtaniya yana samun albashi N204k duk kwanan duniya a matsayin ma'aikacin agaji.

Mutumin ya wallafa wani bidiyo a TikTok don bayar da labarinsa amma ya ce aikin sam babu sauki saboda yana kula da wani tsoho ne.

Asali: Legit.ng

Online view pixel