Tsohon Shugaban Hukumar FIRS Da Tinubu Ya Tsige Ya Magantu

Tsohon Shugaban Hukumar FIRS Da Tinubu Ya Tsige Ya Magantu

  • Tsohon shugaban hukumar tara haraji ta kasa (FIRS), Mohammad Nami, ya yi martani a kan tsige shi da Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi
  • Mutumin mai shekaru 55 ya yi godiya ga tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari da shugaban kasa mai ci Bola Ahmed Tinubu kan ba shi damar hidimtawa kasa
  • Ya ce gwamnatinsa ta tara naira tiriliyan 8 cikin watanni takwas kuma kuma ya ji dadin cika ayyukan sa

FCT, Abuja - Muhammad Nami, tsohon shugaban hukumar tara haraji ta kasa (FIRS), ya yi martani a kan sauke shi da aka yi daga kujerarsa.

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ne ya tsige Nami a ranar Alhamis, 14 ga watan Satumba sannan ya nada mai ba shi shawara ta musamman kan kudaden shiga, Zacchaeus Adedeji, a matsayin mukaddashin shugaban hukumar harajin.

Kara karanta wannan

Dawowarsa Ke Da Wuya, Tinubu Ya Sake Nada Babban Mukami, An Bayyana Sunanta

Tsohon shugaban hukumar FIRS, Muhammad Nami
Tsohon Shugaban Hukumar FIRS Da Tinubu Ya Tsige Ya Magantu Hoto: @NamiMuhammad
Asali: Twitter

A wanni bayan tsige shi, Nami ya fitar da sanarwa inda ya yi godiya ga tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan ba shi damar hidimtawa kasa.

Nami ya kuma mika godiyarsa ga ma'aikatan FIRS wadanda suka yi aiki tare da shi tsawon shekarun.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya rubuta:

“Cike da matukar godiya ga Allah Madaukakin Sarki, ina so in mika sakon godiyata ga tsohon shugaban kasa, Mai Girma Muhammadu Buhari GCFR, da kuma shugaban kasa mai ci, Bola Ahmed Tinubu GCFR, kan damar da aka bani na yi wa kasa da al'umma hidima a matsayin shugaban hukumar tara haraji ta kasa (FIRS) na kusan shekaru hudu.
"Ina son mika tsantsar godiyata ga daukacin ma'aikatan hukumar, masu biyan harajinmu, da kuma yan Najeriya kan yarda da suka yi da ni da maramun baya da bani hadin kai iya lokacin da na yi a mulki."

Kara karanta wannan

Yanzu Yanzu: Shugaban Kasa Tinubu Ya Yi Sabon Nadi Mai Muhimmanci a Hukumar FIRS

FIRS ta tara naira tiliyan 8 cikin wata takwas a karkashin gwamnatina - Nami

Nami ya kuma jaddada nasarorin da ya samu a yayin kula da ragamar harkokin lamura a matsayin shugaban FIRS.

Ya ce gwamnatinsa ta tara naira tiriliyan 8 cikin watanni takwas kuma da za ta sake kafa sabon tarihi na tara akalla naira tiriliyan 13 zuwa karshen shekara.

Nami ya ce zai bar hukumar FIRS a matsayin wanda burinsa ya cika bayan ya cimma duk abubuwan da ya sa gaba a lokacin da yake aiki a matsayin shugaban FIRS.

Ya ce:

"Saboda haka, zan iya cewa zan tafi a matsayin mutum mai cikar buri sanin cewa na yi aiki yadda ya kamata. Zan kuma bar aikin da aka gina bisa inganci na duniya."

Tinubu ya nada Delu Yakubu a matsayin shugabar hukumar NSIPA

A wani labarin, mun ji cewa shugaba Bola Tinubu ya amince da nadin Delu Bulus Yakubu a matsayin shugabar Hukumar Jin Dadin Al'umma ta Kasa (NSIPA).

Kara karanta wannan

Daga Villa Zuwa Gonar Daura: Shehu Ya Bayyana Sabon Aikin Buhari Kwana 100 Bayan Barin Fadar Shugaban Kasa

Wannan nadin nata zai tabbata ne idan majalisar Dattawa ta tantance ta tare da tabbatar da mukamin nata, Legit ta tattaro.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng