Dakarun Sojin Najeriya Sun Sheke 'Yan Ta'addan ISWAP Guda 6 a Jihar Borno
- Gwarazan sojojin Najeriya sun samu nasarar sheƙe yan ta'addan kungiyar ISWAP guda 6 a yankin ƙaramar hukumar Bama ta jihar Borno
- Zagazola Makama ya bayyana cewa yan ta'addan da sojin suka kashe suna da haɗari, su ke dasa bama-bamai a kan hanyoyi
- Gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum, ya kai ziyarar jaje da wasu ƙauyuka da yan Boko Haram suka kashe mutane
Borno - Dakarun sojin rundunar Operation Hadin Kai (OPHK) da ke aikin wanzar da zaman lafiya a Arewa maso Gabas sun sheke mayaƙan kungiyar 'yan ta'addan ISWAP 6 a Banki, jihar Borno
'Yan ta'addan sun gamu da ajalinsu ne a hannun dakarun soji ta musamman tare da haɗin guiwar jami'an Civilian Joint Task Force (CJTF) ranar Alhamis, 22 ga watan Yuni, 2023.
![Sojojin Najeriya sun samu nasara kan ISWAP. Sojojin Najeriya sun samu nasara kan ISWAP.](https://cdn.legit.ng/images/1120/f819fe3120f857fd.jpeg?v=1)
Asali: UGC
Sojojin sun yi wa 'yan ta'addan kwantan ɓauna kana suka samu nasarar aika su lahira a yankin Bula Yobe kuma a titin Darajamal a ƙaramar hukumar Bama ta jihar Borno.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/4f6fc82f994eb5bc.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Zulum Ya Sha Alwashin Daukan Mataki Kan Kisar Gillar Mutum 8 Da ISWAP Ta Yi A Borno
Masani kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a yankin tafkin Chadi, Zagazola Makama, ne ya tabbatar da haka a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Tuwita.
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Ya bayyana cewa 'yan ta'addan da sojojin suka hallaka suna da matuƙar hatsari domin su ke dasa bama-bamai a kan hanyoyi su yi wa jami'an soji kwantan ɓauna.
Mayakan Boko Haram sun kashe matasa 8
Haka nan kuma mayakan Boko Haram sun halaka matasa 8 a yankin kananan hukumomin Mafa da Jere duk a jihar Borno.
Rahoton jaridar Punch ya nuna cewa hudu daga cikin matasan sun fita nemi itacen ƙonawa a Tamsu-Ngamdu lokacin da suka ci karo da 'yan ta'addan.
Gwamnan jihar, Farfesa Babagana Umaru Zulum, ya kai ziyarar ta'aziyya zuwa garuwawan da lamarin ya shafa ɗaya bayan ɗaya ranar Jumu'a.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/06447e61f08f648b.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Sabon Shugaban Rundunar Sojin Najeriya Ya Kama Aiki Gadan-Gadan, Ya Ɗauki Manyan Alkawurra
Zulum ya tabbatar musu da cewa gwamnati ba zata yi ƙasa a guiwa ba wajen kawo karshen matsalar tsaro a faɗin jihar Borno.
Yan Bindiga Sun Kai Sabon Hari Kaduna, Sun Kashe Mutane Sun Sace Matafiya
A wani labarin na daban 'Yan bindiga sun kai sabon kazamin hari kauyen Sabon Layi, ƙaramar hukumar Birnin Gwari a jihar Kaduna.
Bayanai sun nuna cewa 'yan ta'addan sun kashe manoma 3, sun tattara wasu da matafiyan da suka nufi kasuwar mako, sun yi awon gaba da su.
Asali: Legit.ng