Jerin Ministocin Buhari 14 Da Aka Fi Damawa Da Su A Gwamnatin Tarayya Daga 2015 Zuwa Yanzu

Jerin Ministocin Buhari 14 Da Aka Fi Damawa Da Su A Gwamnatin Tarayya Daga 2015 Zuwa Yanzu

  • Yanzu ana makon karshe na gwamnatin Muhammadu Buhari, za a samu canjin gwamnati a Najeriya
  • Daga cikin Ministoci masu barin-gado akwai wadanda sun shafe kusan shekaru takwas da aka yi a ofis
  • Irinsu Rotimi Amaechi da Ogbonnaya Onu sun ajiye aikinsu a 2022, suka nemi takarar shugaban kasa

A rahoton nan, Legit.ng Hausa ta tattaro Ministocin da tun a 2015 ake damawa da su a Gwamnatin Tarayya.

1. Zainab Shamsuna Ahmed

Da farko an nada Zainab Shamsuna Ahmed ne a matsayin karamar Minista, bayan Kemi Adeosun tayi murabus sai ta zama babbar Ministar kudi da tattalin arziki.

Muhammadu Buhari
Ministocin tarayya Hoto: @ Buhari Sallau
Asali: Facebook

2. Mohammed Musa Bello

Tun da aka nada Ministoci a 2015, Malam Mohammed Musa Bello ya zama Ministan birnin tarayya Abuja, a 2019 ne ya samu karamar Minista a ma’aikatarsa.

Kara karanta wannan

FEC: Sunayen Kwamishinonin RMFAC 7 da Aka Rantsar a Taron Karshe a Mulkin Buhari

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

3. Abubakar Malami

Abubakar Malami SAN ya shafe shekaru takwas ya na wakiltar jihar Kebbi a majalisar FEC a matsayin Ministan shari’a kuma babban lauyan gwamnatin kasa.

4. Babatunde Raji Fashola

A duk shekarun nan da aka yi, Babatunde Raji Fashola ne Ministan ayyuka da gidaje na kasa. A wa’adin farko shi ne ya ke kula da ma’aikatar wuta a Najeriya.

5. Rotimi Amaechi

Kafin ya yi murabus domin shiga takara, Rotimi Amaechi ya kasance a gwamnati tun da Muhammad Buhari ya rantsar da Ministocinsa a shekarar farko.

6. Chris Ngige

Chris Ngige ya yi kusan shekaru takwas a kujerar Ministan kwadago da samar da ayyukan yi. Tsohon Gwamnan ya yi niyyar yin murabus a bara, amma ya fasa.

7. Adamu Adamu

Daga cikin Ministocin da ba a canza ba akwai na harkar ilmi, Malam Adamu Adamu. Tun kafin samun mukamin, mutumin Bauchi ya na cikin na kusa da shugaban kasa.

Kara karanta wannan

Buhari Ya Sake Yin Nadin Sababbin Mukamai Ana Saura Kwana 6 a Rantsar da Tinubu

8. Mustapha Baba Shehuri

Wani Minista da watakila ake yawan mantawa da shi a gwamnatin nan shi ne Mustapha Baba Shehuri, ya rike karamin Ministan wutar lantarki da Ministan gona.

9. Ogbonnaya Onu

Da Dr. Ogbonnaya Onu aka kafa gwamnatin nan, zuwa lokacin da ya yi murabus domin shiga takara, ya zama wanda ya fi kowa dadewa a ma’aikatar kimiyya.

10. Osagie Ehanire

A lokacin da Muhammadu Buhari ya nada Ministocin farko, Osagie Ehanire ya zama karamin Ministan lafiya, bayan an dawo karo na biyu sai ya zama babban Minista.

11. Geoffrey Onyeama

A tsawon mulkin nan, Geoffrey Onyeama ne Ministan harkokin kasar waje. Canjin da aka samu kawai shi ne canza mataimakinsa; Khadijah Bukar Abba da Zubairu Dada.

12. Suleiman Adamu

Injiniya Suleiman Adamu Husseini ya yi kusan shekaru takwas ya na rike da kujerar Ministan harkokin ruwa a gwamnatin Muhammadu Buhari, shi ya wakilci Jigawa.

13. Hadi Sirika

Kamar Ministan lafiya, Hadi Sirika ya samu karin matsayi a Agustan 2019 inda aka maida ma’aikatarsa ta jiragen sama ta balle daga karkashin ma’aikatar sufuri.

Kara karanta wannan

Manyan Abubuwa 7 Da Suka Faru Tsakanin 2019 da 2023 a Majalisar Wakilan Tarayyar Najeriya

14. Lai Mohammed

Tsohon sakataren yada labaran APC, Lai Mohammed ne Ministan labarai da al’adu tun 2015, ya na cikin wadanda aka fi damawa da su a gwamnati mai barin-gado.

Asali: Legit.ng

Online view pixel