Pantami da Wasu Ministocin Buhari 9 da Za Su Iya Tsira da Kujerunsu a Mulkin Tinubu

Pantami da Wasu Ministocin Buhari 9 da Za Su Iya Tsira da Kujerunsu a Mulkin Tinubu

  • A ‘yan kwanaki masu zuwa ne Shugaban Najeriya zai sauke daukacin Ministocin gwamnatinsa
  • Watakila a cikin Ministocin kasar akwai wadanda Shugaba mai jiran gado, Bola Tinubu zai tafi da su
  • Wasu Ministoci masu barin-gado sun yi shekaru bakwai a ofis, wasu kuma ba su kai shekara hudu ba

Abuja - A rahoton nan, Legit.ng Hausa tayi kokarin yin hasashe a kan Ministocin Tarayya da za su cigaba da rike mukamansa a sabuwar gwamnati.

1. George Akume

George Akume yana da kyakkyawar alaka da zababben shugaban kasa, ko da bai samu kujerar Minista ba, ana tunanin zai iya samun wata kujera a gwamnatin gobe.

2. Festus Keyamo

Festus Keyamo ya taka rawar gani wajen yakin neman zaben APC, ba abin mamaki ba ne a ga karamin Ministan kwadagon ya cigaba da rike matsayinsa ko waninsa.

Kara karanta wannan

Kwanaki 13 Kafin Ya Bar Aso Villa, Buhari Ya Fadi Kokari 3 da Ya Yi Cikin Shekaru 8

Ministoci
Isa Ali Pantami a taron Ministoci Hoto: Professor Isa Ali Pantami
Asali: Facebook

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

3. Isa Ali Ibrahim Pantami

Idan aka yi la’akari da kokarin da ya yi a ma’aikatar sadarwa da tattalin arzikin zamani da kuma gudumuwar da ya bada a kamfe, Isa Pantami zai iya zarcewa.

4. Ramatu Tijani

Ana rade-radin Ramatu Tijjani ta na so ta rike kujerarta a gwamnati mai zuwa. Hakan zai iya yiwuwa domin sai a 2024 Yahaya Bello zai bar kujerar Gwamna a Kogi.

5. Lai Mohammed

Alhaji Lai Mohammed ya dade tare da Bola Tinubu, watakila ya nemi wani mukami ya ba shi a kujerar jihar Kwara, matsalar kurum ita ce Ministan yana da shekara 71.

6. Olorunnimbe Mamora

Kafin karbar mukami a gwamnatin Muhammadu Buhari, Olorunnimbe Mamora ya yi Sanata a Legas, kuma yana cikin wadanda sun dade da sanin Tinubu a siyasa.

7. Sunday Dare

Idan ana maganar na-kusa da zababben shugaban Najeriyan kafin yau akwai Sunday Dare, watakila a gwamnati mai zuwa a canzawa Ministan matasan ma’aikata.

Kara karanta wannan

Wasu Wurare 4 da Bola Tinubu Zai Iya Shan Wahala Bayan Ya Gaji Muhammadu Buhari

8. Adeniyi Adebayo

Wani da mu ke ganin zai iya samun shiga bayan shudewar gwamnatin nan shi ne Ministan harkokin kasuwanci, masana'antu da hannun jari, Adeniyi Adebayo.

9. Babatunde Fashola

Ko da ya dade yana rike da mukamin Minista, wasu su na hangen Babatunde Fashola a kujerar Ministan shari’a, a matsayinsa na SAN zai iya zama lauyan gwamnati.

10. Abdulrahman Bello Dambazau

Na karshe a jerin shi ne Janar Abdulrahman Bello Dambazau mai ritaya. Duk da ya rasa kujerarsa a 2019, ana ganin tsohon sojan yana tare da shugaba mai jiran gado.

Cikas a gaban Tinubu

A rahoton da mu ka fitar, an ji cewa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu yana shirin karbar mulkin Najeriya a lokacin da ake fama da rashin aikin yi da tsadar kayan abinci.

Tinubu zai nemi cire tallafin man fetur amma hakan zai haifar da tsadar rayuwa. Daga cikin abubuwan da za su ba ciwon-kai akwai samar da isasshen lantarki.

Asali: Legit.ng

Online view pixel