Za a Sake Gudanar da Zabukan Sanata da Na ’Yan Majalisun Tarayya a Jihohi 15 Na Najeriya

Za a Sake Gudanar da Zabukan Sanata da Na ’Yan Majalisun Tarayya a Jihohi 15 Na Najeriya

Za a sake zaben ‘yan majalisun tarayya a gobe Asabar 18 ga watan Maris a mazabun sanata takwas da na ‘yan majalisun tarayya 33 a jihohi 15 na kasar nan.

A cewar hukumar zabe mai zaman kanta (INEC), maimaita zaben kujeru 41 na majalisar dokokin tarayyan za a yi shi ne tare da na gwamnoni da na ‘yan majalisun jiha.

Ba a yi zaben sanata ba a mazabar Enugu East biyo bayan mutuwar dan takarar jam’iyyar Labour kwanaki kadan kafin zaben ranar 25 ga watan Maris, The Nation ta ruwaito.

Hakazalika, ba a yi zaben ba a mazabar Esan Central/Esan West/Igueben a jihar Edo saboda bacewar tambarin daya daga cikin jam’iyyun siyasan kasar nan.

Mazabun da za a sake zabe a gobe Asabar
Kada kuri'u a Najeriya a zaben bana | Hoto: | Hoto: channelstv.com
Asali: UGC

Yadda ta kaya a jihar Sokoto

A jihar Sokoto, an soke zaben mazabun sanata uku da na ‘yan majalisun tarayya 11 saboda ballewar rikici, don haka hukumar zaben ta ce za a sake yin zaben a ranar Asabar.

Kara karanta wannan

Zaben gwamnoni: Jihohi 28 ne za a yi zabe gobe Asabar, ga jerin sunayensu

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

A cewar rahotanni, za a sake zaben na mazabu daban-daban na jihar ta Sokoto da wasu jihohi 14 a Najeriya.

A bangare guda, duk da an ayyana Alhassan Ado Doguwa a matsayin wanda ya lashe zaben dan majalisar tarayya a mazabar Doguwa/Tudun Wada, INEC ta soke nasarar tasa, inda tace an tursasa jami’in zabe ya ayyana shi, Punch ta ruwaito.

Mazabun da za a yi zaben sanata gobe Asabar

  1. Enugu East (Enugu)
  2. Kebbi North (Kebbi)
  3. Plateau Central (Plateau)
  4. Yobe South (Yobe)
  5. Zamfara Central (Zamfara)
  6. Sokoto East, North da South (Sokoto)

Mazabun da za a sake zaben ‘yan majalisun tarayya

  1. Akwa Ibom - Abak/Etim Ekpo/Ika and Ikono/Ini
  2. Edo - Esan Central/Esan West/Igueben and Orhionmwon/Uhunmwode
  3. Imo - Ikeduru/Mbaitoli and Isu/Njaba/Nkwere/Nwangele
  4. Kano - Doguwa/Tudun Wada and Fagge
  5. Kebbi - Arewa/Dandi and Koko/Besse/Maiyoma
  6. Oyo - Ibadan Northeast/Ibadan Southeast and Oluyole
  7. Rivers - Gokana/Khana and Port Harcourt II
  8. Zamfara - Gummi/Bukkuyum and Gusau/Tsafe
  9. Taraba - Takum/Donga/Ussa
  10. Kogi - Bassa/Dekina
  11. Jigawa - Gumel/Maigatari/Sule Tankarkar/Gagarawa
  12. Ebonyi - Ezza North/Ishielu
  13. Bayelsa - Southern Ijaw
  14. Anambra – Igbaru

Kara karanta wannan

Abin da Ya Jawowa Jiga-jigan ‘Yan Majalisa Rasa Kujerunsu a Bana – Gbajabiamila

Idan baku manta ba, a jihohi 28 ne za a yi zaben gwamnoni a Najeriya, kasancewar wasu jihohi tara suna yin zabensu ne a lokaci na daban.

Wannan ya faru sakamakon wasu matsalolin da ke alaka da doka da kuma rikicin kotu na bayan zabuka.

Asali: Legit.ng

Online view pixel