Abun Mamaki: Mabarata a Kaduna Sun ki Karbar Tsohuwar N1,000
- Wasu tarin mabarata da ke bara a titin Kano da ke kwaryar birnin Kaduna, sun ki karbar tsohuwar N1,000 da aka basu sadakar ta
- Wani matashi mai suna Caleb ya sauka daga bas inda ya bude lalitarsa ya mika musu N1,000 amma mabaratan suka watse
- Sun koka da cewa koda ya basu basu san inda za su yi da tsohuwar N1,000 illa iyaka ta zama takardar banza a wurinsu
Kaduna - Wasu gungun mabarata da ke fitaccen titin Kano a jihar Kaduna, sun ki karbar N1,000 da wani matashi ya basu sadaka.
Kamar yadda Daily Post ta wallafa a ranar Laraba, mabarata uku ne suka tunkari matashin mai suna Caleb inda suke neman taimako.
![Mabarata Mabarata](https://cdn.legit.ng/images/1120/50882b615a1d19c3.jpeg?v=1)
Asali: UGC
Yayin da ya sauka daga bas kuma ya yanke hukuncin baiwa mabaratan tsohuwar takardar N1,000 daga lalitarsa.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/2ed0268381d6c96e.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Ya fasa kwai: Tinubu ya fadi makarkashin yin sabbin Naira da karancin mai a Najeriya
Amma cike da mamaki da ya mamaye shi, mabaratan sun koma baya tare da juyawa suka wuce daga wurinsa inda suka ki karbar kudin.
DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar
Matashin yace:
“Mabaratan sun zo wurina suna neman sadaka. Na basu abinda nake da shi amma suka ki karba.”
Caleb yayi bayanin cewa, duk da kokarin da yayi, tsofaffin kudi kadai ne a jikinsa kuma har yanzu bashi da sababbin da suka fito.
Bankuna na cigaba da bayar da tsofaffin kudi duk da umarnin CBN
A wani labari na daban, bankuna a cikin birnin Kano suna cigaba da fitar da tsofaffi kudi a injinansu na ATM duk da kuwa umarnin da babban bankin Najeriya, CBN ya bayar.
A zagayen da aka yi wasu injinan fitar da kudi na bankuna da dama da ke kwaryar birnin Kano, an ga cewa tsofaffin kudaden N1,000, N500 da N200 ke fita.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/1eaa88dd26fb6b35.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Akwai matsala fa: Direbobi a wata jihar Arewa sun cije, sun fadi abin da suke so CBN ta yi
Jama’a sun koka da rashin yalwatar sababbin kudin a gari duk da kuwa babban bankin Najeriyan ya tabbatar da cewa babu gudu balle ja da baya a wa’adin da suka saka ba mayar da tsofaffin kudi takardun kawai.
Hatta ’yan kasuwa a kasuwar Kantin Kwari da ke kwaryar birnin Kano sun koka kan rashin wadatar wannan sabbin kudin hannun jama’a.
Sun bayyana cewa, ba su ga sabbin kudin da yawa a gari ba duk da sauran kwanaki su daina aiki.
Asali: Legit.ng