Bidiyon Yaro Makanike Na Zuba Turanci Ya Ba Jama’a Mamaki

Bidiyon Yaro Makanike Na Zuba Turanci Ya Ba Jama’a Mamaki

  • Wani yaro dan Najeriya mai suna Mubarak ya siye zukatan jama'a a TikTok yayin da aka ga bidiyonsa yana zabga turanci
  • A gajeren bidiyon da aka yada, an ga Mubarak sanye da yagaggun tufafin aikin kanikanci yana tafka muhawara kan wani maudu'i
  • Kalaman Mubarak sun ba 'yan TikTok mamaki, sun shiga mamamkin dalilin da yasa yaron baya zuwa makaranta

Dandazon mutane a shafin TikTok sun kamu da kaunar wani yaro mai suna Mubarak saboda irin kwazon da yake dashi.

Hakan ya fara ne daga wani bidiyon da @ayofeliberato ya yada na lokacin da Mubarak ke karanta wata muhawara da ta dauki hankali ya yadu a intanet.

Kwarewarsa a yaren turanci ta ba jama'a mamaki, wannan yasa suka ce ya yi matukar burge su.

Mustapha, makanike dake zuba turanci
Bidiyon Yaro Makanike Na Zuba Turanci Ya Ba Jama’a Mamaki | Hoto: TikTok/@ayofeliberato
Asali: UGC

Mubarak, wanda yaro ne a shagon masu sana'ar kanikanci yana muhara ne kan yin karatu da rana a madadin dare.

Kara karanta wannan

Gwamna ya yi karin haske kan bidiyonsa da aka gani yana umartar sojoji su zane ma'aikata a jiharsa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya kawo hujjojinsa masu daukar hankali, inda ya ce dare mahutar bawa ce, don haka babu batun karatu da dare, sai dai da rana.

Kalli bidiyon:

Me yasa Mubarak ba ya zuwa makaranta?

Bayan ganin bidiyon, da yawan jama'a a TikTok sun shiga mamakin dalilin da yasa yaro mai kwazo kamar Mubarak ba a ganshi a makaranta ba.

Sun bayyana bukatar dalilin da yasa yaron ke zuwa wurin gyare-gyaren injuna a madadin makaranta don karatu.

Ba a dai tabbatar ba ko yaron ba ya zuwa makaranta kwata-kwata, ko kuma yana aikin kanikanci ne a lokutan hutu ko karshen mako.

Ga dai kadan daga abin da mutane ke cewa:

@bhadboi Nel$ yace:

"Irin wadannan ne yaran da peter obi zai tallafawa."

@fortunecedric yace:

"Don Allah ya kamata wannan bidiyon ya yadu sosai."

@Elubod yace:

Kara karanta wannan

Wani Dan Wasa a Najeriya Ya Yanke Jiki Ya Fadi, Ya Mutu Ana Tsaka da Buga Kwallo

"Me yasa yake koyon sana'ar kanikanci."

@user1200126718789 yace:

"Allah ya yi maka albarka yaro. Ina matukar alfahari da kai saboda wannan."

@user1923428674135 yace:

"Allah ya yiwa duk hazikai a Najeriya albarka.

@Sammy Osaretinmwen Uwaifo yace:

"Wannan wani babban haziki za a yi a nan gaba."

@Yvonne yace:

"Wayyo, yana bata basirarsa a nan. Allah ya turo mai taimakonsa."

@Kazeem Adigun yace:

"Abin mamaki. A ina wannan yaron yake?"

@dotuna3 yace:

"Ya kamata wannan yaron ya ci gaba da karatu don Allah."

@attehdaniel yace:

"Ya kamata ya samu tallafin karatu."

Dalibar Jami’a a Najeriya Ta Samu Karuwa, Ta Haifi ’Ya’ya Biyar a Lokaci Daya

A wani labarin, Oluomachi Nwoye, dalibar ajin karshe a jami'ar ilimin noma ta Michael Okpara ta samu karuwar jarirai biyar a rana daya a asibitin tarayya na Umuahia a jihar Abia.

Mahaifiyar Oluomachi ta ce jariran biyar da diyarta ta haifa sun hada da maza biyu da mata uku, kuma ta haihu ne da misalin karfe 9:15 na dare.

Kara karanta wannan

Lambar Girma: Yadda Ake ta Surutu Yayin da Manyan Na-kusa da Buhari Suka Tashi da Matsayi

A wani rahoton Vanguard, an ce biyu daga jariran kuma maza na karbar kulawa ta musamman kasancewar an haife su da 'yar matsala.

Asali: Legit.ng

Online view pixel