Buhari Zai Karrama Sarkin Kano, Sarkin Zazzau Da Wasu Sarakuna 18 Da Lambar Girma Ta Kasa

Buhari Zai Karrama Sarkin Kano, Sarkin Zazzau Da Wasu Sarakuna 18 Da Lambar Girma Ta Kasa

  • Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai karrama mutane fiye da 400 da lambar girmamawa ta kasa na 2022
  • Daga cikin wadanda za a girmama akwai manyan jami’an gwamnati, sarakunan gargajiya, manyan masu fada aji da sauransu
  • Sai dai kuma, sarakuna 20 ne suka kai matakin karshe inda Ooni na Ife, da sarkin Kano ke kan gaba a rukunin

An saki jerin sunayen mutanen da gwamnatin Najeriya za ta karrama da lambar girmamawa ta kasa na wannan shekarar.

Legit.ng ta rahoto cewa mutane 437 ne za su samu lambar yabo daga bangarori daban-daban na rayuwa kama daga yan siyasa, yan kasuwa, jami’an gwamnati, sarakunan gargajiya da kuma masu nishadantarwa.

Sarakuna
Buhari Zai Karrama Sarkin Kano, Sarkin Zazzau Da Wasu Sarakuna 18 Da Lambar Girma Ta Kasa Hoto: Ooni of Ife, Emir of Kano, Olu of Warri, Oba of Benin
Asali: UGC

Lambar yabon wannan shekarar ya hada da GCON biyar, CFR 54, CON 67, OFR 64, OON 101, MFR 75, MON 56 da FRM 8.

Kara karanta wannan

Buhari zai karrama Abba Kyari, Tunde, Okonjo-Iweala da Wasu 437 da Lambar Girma

Shugaba Buhari zai gabatarwa kowani mutum da nasa kason lambar girmamawan a fadar shugaban kasa a ranar Talata, 11 ga watan Oktoba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A wannen zauren, Legit.ng ta lissafo wasu daga cikin sarakunan da suka samu shiga sahun wadanda za a karrama a wannan shekarar inda su 20 zasu samu lambar yabo ta CFR.

Ga jerin sunayen sarakunan da aka lissafa za a karrama a kasa:

SUNAMATSAYIJIHALAMBAR YABO
1Mai martaba Oba Adeyeye Enitan Ogunwusi Ojaja IIOoni na IfeOsunCFR
2HM Omo N'Oba N'Edo Uku Akpolokpolo EwuareOba na BeninEdoCFR
3Mai martaba, Alhaji Aminu Ado BayeroSarkin KanoKanoCFR
4Mai martaba Ahmed Nuhu Bamali Sarkin Zazzau Kaduna CFR
5Mai martaba Prof James Ortese Ayatse Tor Tiv V BenueCFR
6Mai martaba Abubakar Shehu Abubakar III Sarkin GombeGombeCFR

Kara karanta wannan

Shugaba Buhari Ya Karrama Buratai Da Babban Lambar Yabo Na Kasa

7Mai martaba Alh. Muhammadu ibn Abali Muhammad Idrissa Sarkin FikaYobeCFR
8Da. Jacob Gyang BubaGbong Gwom Jos PlateauCFR
9Mai martaba Justice Sidi Bage Muhammad I (JSC Rtd) Sarkin LafiaNasarawaCFR
10Mai martaba King Dandeson Douglas JAJA King Jaja na Opobo RiversCFR
11Mai martaba Oba Gabriel AdejuwonOnisan na Isan EkitiCFR
12Mai martaba Oba (Dr) Aladetoyinbo Ogunlade Aladelusi, Odundun II Deji na AkureOndoCFR
13Mai martaba Oba Babatunde Adewale AjayiAkarigbo na RemoOgunCFR
14Mai girma Ntenyin (Dr) Solomon Daniel Etuk, JPOku Ibom Ibibio Akwa IbomCFR

15Mai martaba Igwe Amb. Lawrence AgubuzuIgwe na Eziama EnuguCFR
16Mai martaba King Alfred Diete-SpiffShugaban majalisar sarakunan BayelsaBayelsaCFR
17Mai martaba Ogiame Atuwatse III Olu na WarriDeltaCFR
18Mai martaba Eze (Dr) E. C. OkekeShugaban majalisar sarakunan ImoImoCFR
19Mai martaba Eze Joseph Ndubuisi Nwabeke Shugaban majalisar sarakunan AbiaAbiaCFR
20Mai martaba HRM Eze Charles N. NkpumaCiyaman, EbonyiEbonyiCFR

Kara karanta wannan

Zaben 2023: Ku Sake Bawa APC Wata Damar, In Ji Dr Kailani Muhammad

Shugaba Buhari Ya Karrama Buratai Da Babban Lambar Yabo Na Kasa

A gefe guda, mun ji cewa tsohon babban hafsan sojojin kasan Najeriya kuma jakadan Najeriya a Jamhuriyar Benin, T.Y. Buratai ya shiga jerin wadanda za su samu lambar yabo ta kasa na 'Commander of the Order of the Federal Republic', (CFR).

Tsohon shugaban sojojin da wasu fitattun yan Najeriya guda 436 ne za a karrama da lambar yabon a wannan shekarar.

Kamar yadda Legit.ng ta gano, Shugaba Muhammadu Buhari, a ranar Talata 11 ga watan Oktoba zai gabatar da lambar yabon da wadanda aka zaba a gidan gwamnati, Abuja.

Asali: Legit.ng

Online view pixel