Shugabar Kotun Ɗaukaka Ƙara, Mai Shari'a Monica, Ta Yi Rashin Wani Ɗanta

Shugabar Kotun Ɗaukaka Ƙara, Mai Shari'a Monica, Ta Yi Rashin Wani Ɗanta

  • A karo na biyu, ɗan shugabar Kotun ɗaukaka ƙara a Najeriya, Mai shari'a Monica, ya rasu daga kwanciya bacci ranar Asabar
  • Bayanai sun tabbatar da cewa marigayin wanda ya karanci lissafi, yana aiki ne da ma'aikatar sufuri ta ƙasa a jihar Legas kamin rasuwarsa
  • A shekarar 2011, Mai shari'a ta rasa babban ɗanta na fari, wanda ya rasu bayan wani direban daki ka tsere ya kaɗe shi a Jos, jahar Filato

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Abuja - Shugabar Kotun ɗaukaka ƙara ta Najeriya, Mai shari'a Monica Dongban-Mensem, ta ƙara yin wani babban rashi na ɗanta, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Ɗan da ta haifa na biyu, Prince Paeke Shapnaan Dongban, ɗan kimanin shekara 38 a duniya ya rasu yana cikin bacci da safiyar ranar Asabar.

Mai Shari'a Monica Dongban-Mensem.
Shugabar Kotun Ɗaukaka Ƙara, Mai Shari'a Monica, Ta Yi Rashin Wani Ɗanta Hoto: dailytrust.com
Asali: UGC

Wata majiya ta tabbatar da rasuwar ga manema labarai da cewa tuni iyalan gidan Alkalin suka shiga cikin duhu da jimamin wannan rashi.

Kara karanta wannan

Mambobi 20,000 sun sauya sheƙa zuwa APC a jiha ɗaya, Shugabar mata ta rungume su hannu biyu

Marigayin, wanda ya karanci darasin Lissafi (BSc Mathematics) a jami'ar fasaha ta tarayya da ke Minna, jihar Neja, ya na aiki ne a ma'aikatar Sufuri ta ƙasa a jihar Legas lokacin rayuwarsa.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Yadda Mai Shari'an ta rasa ɗanta na fari

Wannan rasuwa na zuwa ne shekaru 11 bayan mutuwar ɗan shugabar Kotun na fari watau Kwapda’as Rangna’an Samson Dongban.

Ɗanta na farko ya mutu ne bayan wani direban daki ka tsere ya kaɗe shi a Jos, babban birnin jihar Filato, a shekarar 2011, the nation ta ruwaito.

Sai dai bayan rasuwarsa, Mai Sharia Monica, ta kafa gidauniyar kare haɗurra, 'Kwapda’as Road Safety Demand Foundation' domin tuna wa da babban ɗan ta.

A wani labarin na daban kuma kun ji cewa 'Yan bindiga sun yi garkuwa da wani Babban Malami a mahaifar gwamnan Sakkwato

Kara karanta wannan

Shugaba Buhari ya aike da muhimmin saƙo ga shugaban jam'iyyar APC na ƙasa

Kwanaki kaɗan bayan ɓinne Malamin Majami'ar Katolika, wanda aka sace kuma aka kashe shi a jihar Kaduna, yan bindiga sun sake garkuwa da wani a Sakkwato.

Wasu miyagun yan bindiga da ba'a gane ko su waye ba sun yi garkuwa da Malamin Coci, Tony Udemezue, wanda ke ƙarƙashin Cocin Ƙatolika na jihar Sakkwato.

Asali: Legit.ng

Online view pixel