'Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Malamin Coci A Mahaifar Gwamnan Sokoto

'Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Malamin Coci A Mahaifar Gwamnan Sokoto

  • Miyagun yan bindiga sun yi garkuwa da wani Fadan cocin Katolika a garin Tambuwal da ke yankin jihar Sakkwato
  • Bayanai sun nuna cewa Malamin cocin ya sanar da yan sanda haɗarin da ke shirin faruwa da shi, amma ba su kai masa ɗauki ba
  • Daraktan sadarwa na Coci-Cocin Katolika a Sakkawato ya roki a sa Malamin da iyalansa cikin Addu'a

Sokoto - Kwanaki kaɗan bayan ɓinne Malamin Majami'ar Katolika, wanda aka sace kuma aka kashe shi a jihar Kaduna, yan bindiga sun sake garkuwa da wani a Sakkwato.

Wasu miyagun yan bindiga da ba'a gane ko su waye ba sun yi garkuwa da Malamin Coci, Tony Udemezue, wanda ke ƙarƙashin Cocin Ƙatolika na jihar Sakkwato.

Taswirar jihar Sakkwato.
'Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Malamin Coci A Mahaifar Gwamnann Sokoto Hoto: vangaurdngr.com
Asali: UGC

Jaridar Vanguard ta tabbatar a rahotonta cewa an sace Malamin cocin ne a awannin wayewar garin Litinin a gidansa da ke garin Tambuwal, mahaifar gwamna Aminu Waziri Tambuwal a jihar Sokoto.

Kara karanta wannan

APC Ta Samu babban Naƙasu a Kaduna, Manyan Jiga-Jigai 15 Sun Fice Daga Jam'iyyar

Daraktan sadarwa na ƙungiyar Malaman Coci-Cocin Katolika a Sakkwato, Rabaran Fr. Chris Omotosho, ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai ranar Litinin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Fr. Omotosho ya ce:

"Ɗaya ɗaga cikin Malaman Cocin mu a Tambuwal, jahar Sakkwato, Tony Udemezue, ya shiga hannun masu garkuwa da mutane a gidansa (mahaifar mai girma gwamnan jihar, Aminu Tambuwal).
"Ba bu wani jami'in hukumar yan sanda guda ɗaya da ya kawo ɗauki awa ɗaya kenan (tun karfe 2:00 na dare, wayewar garin Litinin) duk da ya kira ya sanar da su ta wayar salula kafin a yi awon gaba da shi.".
"Dan Allah mu daure mu jure sanya shi da iyalansa cikin Addu'o'in mu."

An kama hatsabibin mai garkuwa

A wani labarin kuma an kama wani ƙasurgumin mai garkuwa yana ɗaukar ma'aikata zasu sace mahaifin kwamishina a Neja

Kara karanta wannan

Tsautsayi: Kwata ta yi ajalin wani matashi ɗan shekara 25, Ghaddafi Saleh, a Kano

Hukumar yan sanda reshen jihar Neja ta ce ta kama wani kasurgumin mai garkuwa da ke shirin sace manyan mutane biyu a jihar.

Yayin bincike, wanda ake zargi Alhaji Bashiru ya amsa cewa yana shirin sace su ne saboda bashin kudin da yake bi.

Asali: Legit.ng

Online view pixel