Innalillahi: Wani jirgin sama da ya dauko 'yan sanda ya yi hatsari a Bauchi

Innalillahi: Wani jirgin sama da ya dauko 'yan sanda ya yi hatsari a Bauchi

  • Rahoton da muke samu ya bayyana cewa, an samu wani hadarin jirgin saman 'yan sanda a wani yankin jihar Bauchi
  • An ce jirgin ya taso ne daga babban birnin tarayya Abuja, inda ya samu matsala ya yi hadari a filin jirgin Bauchi
  • Sai dai, cikin godiyar Allah ba a samu mutuwa ba, amma wasu mutane da jirgin ya dauko sun samu raunuka

Bauchi - Gidan talabijin na Channels ta ruwaito cewa, wani jirgin sama mai saukar ungulu na ‘yan sanda da ya taso daga Abuja ya yi hatsari a filin tashi da saukar jiragen sama na Bauchi, Hukumar Binciken Hatsari ta bayyana a ranar Alhamis.

Sai dai, ba a sami asarar rai ba, in ji rahoton na AIB.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Buhari ta amince a bada kwangilolin wasu tituna 16 da za su ci Naira Biliyan 64

Jirgi ya yi hadari a Bauchi
Innalillahi: Jirgin sama mai saukar ungulu na 'yan sanda ya yi hatsari a Bauchi | Hoto: thenationonlineng.net
Asali: UGC

A cewar sanarwar da The Nation tace ta samo:

“A ranar 26 ga Janairu, 2022, Hukumar Kula da Jiragen Sama ta Najeriya (NAMA) ta sanar da Ofishin Binciken Hatsarin Hatsari, Najeriya game da wani hatsarin da ya rutsa da wani jirgin sama mai lamba Bell 429 mai lamba 5N-MDA mallakin rundunar ‘yan sandan Najeriya (NPF).

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

“Hatsarin ya faru ne a ranar 26 ga watan Janairu, 2022 da misalin karfe 7:30 na yamma a filin jirgin saman Bauchi.
“Jirgin na NPF ya taso ne da misalin karfe 16:54 UTC zuwa Bauchi tare da mutane shida a cikcinsa da nisan 5,500ft.
“An samu wasu da suka ji raunuka amma babu mutuwa.
“Hukumar binciken, AIB-N tana bukata kuma tana neman taimakon ku. Muna son jama'a su sani cewa za mu so samun faifan bidiyo, shaida, ko bayanan da jama'a suka iya samu na hadarin da zai iya taimaka mana da wannan binciken.

Kara karanta wannan

Da dumi-dumi: Sojoji sun kame 'yan daba cikin mota gabanin zaben gwamnan Ekiti

Wani jirgin saman Arik daga Legas ya yi hadari, ya sauka a Asaba

A wani labarin, daya daga cikin kamfanonin jiragen saman Najeriya, Arik Air da ya tashi daga Legas zuwa Asaba kana ya yi hatsari a wani yanki mai nisa a babban birnin jihar Delta da ke Kudu maso Kudu.

Rahotanni sun nuna cewa sama da fasinjoji 25 ne suka shiga jirgin da misalin karfe 6 na yamma a filin jirgin saman Murtala Mohammed da ke jihar Legas a kudu maso yammacin Najeriya.

AIT ta ce ta yi kokarin tabbatar da labarin daga mahukuntan kamfanin amma hakan bai samu ba. Sai dai daya daga cikin jaruman fina-finan Nollywood, Uche Elendu, wacce tana daya daga cikin fasinjojin ta ce sun tsallake rijiya da baya.

Asali: Legit.ng

Online view pixel