Daga karshe: An sako shugaban ASUU da tsohon dan takarar gwamna da aka sace

Daga karshe: An sako shugaban ASUU da tsohon dan takarar gwamna da aka sace

  • Wasu masu garkuwa da mutane sun sako shugaban ASUU reshen jihar Filato da suka sace kwanakin baya
  • Hakazalika, sun kuma sako wani tsohon dan takarar gwamnan jihar da aka sace su tare da shugaban na ASUU
  • Rahotanni sun ce an biya kudaden fansa kafin a sako su kamar yadda masu garkuwar suka nema a farko

Jihar Filato - Rahoton Premium Times ya ce, masu garkuwa da mutane sun sako shugaban kungiyar malaman jami’o’i (ASUU), reshen jami’ar jihar Filato, Hassan Zitta, da tsohon dan takarar gwamna a jihar, Nicholas Nshe.

Sakataren kungiyar, Samson Deme ne ya tabbatar da hakan ga jaridar ta wayar tarho, ya ce an sako mutanen biyu ne a daren ranar Talata bayan sun shafe kwanaki 11 a wurin masu garkuwa da mutane.

Mista Deme ya kara da cewa, akalla an biya kudin fansa naira miliyan 10 kafin a sako su.

Kara karanta wannan

Hotunan yadda ginin wurin Ibada ya hallaka mutane suna tsaka da bautar Allah

An sako shugaban ASUU da tsohn da takarar gwamnan da aka sace
Yanzu-Yanzu: An sako shugaban ASUU da tsohon dan takarar gwamna da aka sace | Hoto: thenationonlineng.net
Asali: UGC

A baya Punch ta rahoto cewa masu garkuwa da mutanen, sun yi watsi da kudi N7m a matsayin kudin fansan Nshe.

Mutanen biyu sun shafe kwanaki 11 tare da wadanda suka sace su bayan an yi garkuwa da su a jajibirin sabuwar shekara a gidan tsohon dan takarar gwamna kuma tsohon shugaban karamar hukumar Shendam, Mista Nshe.

Mista Deme ya ce:

“Yayan ya ce bayan an biya Naira miliyan 10 ba a sake su ba. Sai da suka kara wasu kudi domin a sake su amma ban san nawa ba."

An samu labarin cewa masu garkuwan sun bukaci kimanin Naira miliyan 90 – Naira miliyan 50 ga tsohon dan takarar gwamnan da kuma Naira miliyan 40 ga shugaban ASUU domin a sako su.

Ya zuwa yanzu dai ba a samu jin ta bakin Ubah Ogaba, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Filato ba.

Kara karanta wannan

Da dumi-dumi: Bayan watanni 6, an sako daliban kwalejin da aka sace a Kebbi

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da wani dan jarida, Salisu Maki, a Nasarawa

A wani labarin, wasu ‘yan bindiga wadanda sun kai 9 a ranar Talata, sun yi garkuwa da wani dan jarida wanda ma’aikaci ne da Nasarawa Broadcasting Service, Salisu Maki a Lafia, babban birnin jihar, Vanguard ta ruwaito.

Sun sace Maki ne da misalin karfe 9:30 na safiyar Talata a gidansa da ke kan titin Akurba a karamar hukumar Lafia yayin da ya ke hanyarsa ta komawa gida daga aiki.

Ganau sun shaida yadda ‘yan bindigan su ka afka har wuraren gidan Maki su na harbe-harbe inda su ka tsorata jama’a daga nan su ka yi garkuwa da mutumin.

Asali: Legit.ng

Online view pixel