Kasar Sin zata bude bankuna a Najeriya, wannan shine yarjejeniyar da mukayi: Jakadan Beijing

Kasar Sin zata bude bankuna a Najeriya, wannan shine yarjejeniyar da mukayi: Jakadan Beijing

  • Gwamnatin kasar China zata budewa bankunanta a Najeriya kuma zasu fara aiki nan ba da dadewa ba, cewar Jakadanta
  • Hakazalika bankunan Najeriya zasu iya bude rassa a kasar Sin kuma su rika gudanar da ayyukansu
  • Jakadan yace wannan na cikin abubuwan da aka amince dasu yayin yarjejeniyar canjin kudi tsakanin Najeriya da Sin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

FCT Abuja - Jakadan kasar Sin dake Najeriya, Mr Cui Jianchun, ya bayyana cewa nan ba da dadewa ba gwamnatin kasarsa zata budewa bankuna a Najeriya.

Ya kuma bayyana cewa hakazalika za'a iya bude bankunan Najeriya a Sin, inda yace wannan na cikin abubuwan da suka wajaba ayi don tabbatar da yarjejeniyar canjin kudi tsakanin Najeriya da Sin ta yiwu.

Jakadan Sin, ya ce yanzu haka yana aiki tukuru don ganin cewa bankuna kasarsa su fara aiki a Najeriya, hakazalika na Najeriya a kasar Sin.

ThisDay ta ruwaito cewa ya bayyana hakan ne ranar Talata a Abuja ga manema labaran yayin jawabi kan nasarorin da aka samu kan shirin canjin kudi tsakanin Najeriya da Sin.

Kara karanta wannan

Ana shirin cafke Tinubu idan ya je Amurka? Jakadan Najeriya ya yi bayani

Jianchun yace za'a fadada shirin daga N750 billion da akayi a bayan.

Kasar Sin zata bude bankuna a Najeriya, wannan shine yarjejeniyar da mukayi: Jakadan Beijing
Kasar Sin zata bude bankuna a Najeriya, wannan shine yarjejeniyar da mukayi: Jakadan Beijing Hoto: Aso Villa

A cewarsa:

"Manyan bankunan kasashenmu biyu ke aiwatar da yarjejeniya. Ana samun nasara kuma ina kokarin ganin bankunan Sin sun zo Najeriya kuma Najeriya su fara aiki a Sin.

Rahoton ya kara da cewa Jakadan yace zai so yan majalisun Najeriya su fara mu'amala da yan majalisun Sin yayinda ake shirin taron zuba jarin Sin da nahiyar Afrika da zai gudana a Nuwamba a kasar Senegal.

Ma'aikatar Lafiya na shirin karban bashin N82bn don sayen ragar kariya daga cizon sauro

A bangare guda, Majalisar dattawar Najeriya ta yi Alla-wadai da shirin da ma'aikatar kiwon lafiyan Najeriya ke yi na karban bashin $200 million (N82,070,388,916.76) a kasafin kudin shekarar 2022.

Ma'aikatar za ta amfani da wannan bashi ne wajen sayawa yan Najeriya ragar kariya daga cizon sauro, rahoton SR.

Sakaraten din-din-din na ma'aikatar ya bayyanawa kwamitin a taron bayani kan kudin da ma'aikatar ta bukata cikin kasafin kudin 2022.

Kara karanta wannan

Tinubu zai yi magana gaban shugabannin kasashen duniya a Amurka, an sanya lokaci

Daya daga cikin mambobin kwamitin kiwon lafiya na majalisar dattawa, Gershom Bassey, ranar Talata ya ce sam ba dashi za'a yi wannan ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and leads the Hausa Desk at Legit.ng. He is AfricaCheck's ambassador and HumAngle Technology and Civic Impact Fellow. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. His commitment to excellence has earned him recognition, including the Legit Fearless Team Player of the Year 2023 and 2024 Distinguished Editorial Leadership Award. Email: salisu.ibrahim@corp.legit.ng