Latest
Rahotanni sun bayyana cewa Ƙasar Masar ta rasa alhazai 600 waɗanda suka rasu sakamakon tsananin zafin da aka yi fama da shi a aikin hajjin bana a Saudiyya.
Matsakaicin farashin man fetur a watan Mayun 2024 ya kai N769.62, wanda ke nuni da karuwa idan aka kwatanta da farashin da aka saye shi a watan Mayun 2023 (N238.11).
Babbar Kotun Tarayya ta yi hukunci kan dambarwar masarautun jihar Kano tsakanin Sanusi II da Aminu Ado Bayero a yau Alhamis 20 ga watan Yunin 2024.
Sarkin masarautar Akinale a jihar Ogun, Oba Olufemi Ogunleye ya riga mu gidan gaskiya bayan fama da gajeruwar rashin lafiya a asibitin Landan ranar Laraba da yamma.
Alhaji daga jihar Jigawa ya ƙara ɗaga kimar Najeriya yayin da ya mayar da jakar kuɗin da ya tsinta a Masallacin Annabi SAW a Madinah, ya yi cigiya bai ga mai ita ba.
Rahotanni sun tabbatar da cewa wani soja ya hallaka farar hula a birnin tarayya Abuja. Sojan ya yi wannan ta'asar ne bayan gardama ta barke tsakaninsu a kasuwa.
Kungiyoyin ma’aikatan jami’o’in Najeriya sun ba gwamnatin tarayya wa’adin mako biyu da ta biya su albashin watanni hudu da ta rike ko ta fuskanci fushin kungiyoyin.
Najeriya ta sake babban rashi bayan rasuwar Hajiya a kasar Saudiyya mai suna Ramota Bankole wacce ta kasance jajirtacciya a jam'iyyar APC da ta rike mukamai.
An fara shiga fargaba a Kano bayan da Babbar Kotun Tarayya ta yanke hukunci kan halaccin dokar da ta rusa masarautun jihar guda biyar da kuma nadin Sanusi II.
Masu zafi
Samu kari