An 'Gano' Waɗanda Suka Taimaka wa Isra'ila da Amurka har Aka Hallaka Khamenei
- Rahotanni sun bayyana yadda hukumar leken asiri ta CIA ya ba da gudunmawa wurin farmaki kan Ayatullah Ali Khamenei
- Majiyoyi sun ce bayanan sirri sun taimaka wa Amurka da Isra’ila kashe jagoran Iran, Ayatollah Ali Khamenei, a harin Tehran
- An ce CIA ta dade tana bibiyar Khamenei, inda ta gano taron manyan jami’an tsaro da aka shirya a wani katafaren wuri domin tattauna halin da ake ciki
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Tehran, Iran - Wani rahoto ya bayyana cewa bayanan sirri na CIA sun taimaka wajen jagorantar hare-haren da Amurka da Isra’ila.
Harin da aka kai ya taimaka wurin hallaka jagoran addinin Musulunci a Iran, Ayatullah Ali Khamenei wanda ya jawo jimami a kasar.

Source: Getty Images
Rawar da CIA ta taka a kisan Khamenei
Rahoton jaridar The New York Times ya ce CIA ta gano cewa Ayatollah Ali Khamenei zai halarci wani muhimmin taro da manyan jami’an Iran.
An ce hukumar leken asirin Amurka ta shafe watanni tana bibiyar motsinsa, inda ta gano taron zai gudana safiyar Asabar a Tehran.
Asali Amurka da Isra’ila sun shirya kai harin da dare, amma sun sauya shirin bayan samun bayanan sirri daga CIA.
An bayyana cewa Amurka ta mika bayanan ga Isra’ila, wadda ta tsara yadda za a kai harin kan shugabannin Iran.
Rahoton ya ce an fara aikin ne da misalin karfe shida na safe a Isra’ila, inda makamai masu linzami suka fada sansanin.
Da misalin karfe 9:40 na safe, makamai masu linzami masu nisa suka lalata wurin taron da ke tsakiyar Tehran wanda ya jawo suka daga kasashe daban-daban.

Source: Twitter
Manyan jami'an tsaron Iran da suka rasu
Baya ga kisan Khamenei da aka yi a Tehran, an kashe shugaban rundunar IRGC, Janar Mohammad Pakpour, da mai ba da shawara Ali Shamkhani
Sannan an hallaka Ministan tsaron Iran, Aziz Nasirzadeh da kuma shugaban ma'aikatan sojojin Iran, Janar Abdolrahim Mousavi da wasu daga cikin iyalansa.
Hukumar shari’ar Iran ta tabbatar da mutuwar manyan jami’an, yayin da kasar ta fara daukar matakin ramuwar gayya.
An ruwaito cewa Iran ta kai hare-hare a yankin Gulf, ciki har da Abu Dhabi da kusa da sansanonin sojojin kasar Amurka.
Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce hare-haren sojin Amurka za su ci gaba muddin ya zama dole domin kare kansu daga barazanar Iran.
Ana jimamin mutuwar Ali Khamenei a Iran
Mun ba ku rahoton cewa dubban mutane sun taru a birnin Tehran suna makokin kisan Ayatollah Ali Khamenei bayan harin hadin gwiwar Amurka da Isra’ila.
Rundunar IRGC ta sha alwashin daukar mummunan ramuwar gayya kan Isra’ila da sansanonin Amurka a yankin Gulf yayin da ake ci gaba da zaman dar-dar a yankin.
Shugaba Donald Trump ya gargadi Iran cewa duk wata ramuwar gayya za ta jawo hari mafi tsanani da ba a taba gani ba inda ya ce ba zai sassauta masu ba ko kadan.
Asali: Legit.ng

