An Gayyaci Manyan Malaman Musulunci 2 daga Najeriya, Za Su Yi Jawabi a Birtaniya

An Gayyaci Manyan Malaman Musulunci 2 daga Najeriya, Za Su Yi Jawabi a Birtaniya

  • Tsohon Ministan Sadarwa, Sheikh Isa Ali Pantami da shugaban Izala na Najeriya, Abdullahi Bala Lau za su yi jawabi a Birtaniya
  • Manyan malumman guda biyu za su halarci taron shekara-shekara na kungiyar musulmin Najeriya mazauna Birtaniya
  • Ana sa ran masana, kwararru da shugabanni za su halarci taron wanda zai gudana gobe Lahadi, 26 ga watan Oktoba, 2025

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Manchester, Birtaniya – Kungiyar Musulmin Najeriya mazauna kasar Birtaniya sun gayyaci manyan malaman sunnah domin su gabatar da jawabi a taron shekara-shekara

Taron kungiyar musulmin mai suna Nigeria Muslim Forum UK (NMFUK) zai gudana ne ranar Lahadi, 26 ga watan Oktoba, 2025 a birnin Manchester na kasar Ingila watau Birtaniya.

Kara karanta wannan

Abin da ya sa wasu gwamnoni da kusoshin Arewa ke son Turaki ya zama shugaban PDP

Sheikh Isa Pantami.
Hoton tsohon Ministan Sadarwa, Farfesa Isa Ali Pantami Hoto: Prof. Isa Pantami
Source: Facebook

Isa Pantami zai yi jawabi a Manchester

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani na Najeriya, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, shi ne babban bako mai jawabi a taron.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Taron na bana mai taken “Ethical Digital Economy: The Future of Community-Centred Islamic Digital Banking” zai mayar da hankali ne kan dangantakar dake tsakanin fasahar zamani, ɗabi’a, da tsarin kuɗin Musulunci a wannan zamani.

Pantami, babban malamin Sunnah a Najeriya zai yi jawabi a wurin wannan taro da zai gudana gobe Lahadi.

An gayyaci Sheikh Abdullahi Bala Lau

Sauran manyan baki da za su yi jawabi sun haɗa da Sheikh Abdullahi Bala Lau, shugaban Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS) wacce aka fi sani da Izala.

Haka kuma Mr Raza Ullah, wanda shi ne Shugaba kuma wanda ya kafa Pfida, wani dandali na harkokin kudin halar, ethical finance da ke jan hankalin duniya, zai yi jawabi a wurin.

Kara karanta wannan

Fasahar AI za ta kawo matsala a ayyukan mutane? Sheikh Isa Pantami ya yi bayani

Taron zai samu halartar manyan masana, shugabanni, da kwararru a fannin fasaha da kuɗi, domin tattauna hanyoyin da za a iya amfani da fasahar zamani wajen gina tsarin kuɗi na Musulunci da ya dace da ka’idojin ɗabi’a da adalci.

Hakan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar NMFUK, Dr Bilyaminu Romo ya fitar kan abubuwan da suka tsara a taron wannan shekara.

Abubuwan da taron NMFUK ya kunsa

Ya bayyana cewa jawabin Farfesa Pantami zai mai da hankali ne kan rawar da kirkire-kirkiren fasaha za su taka wajen faɗaɗa harkokin kuɗi a Musulunci a Najeriya.

A rahoton Guardian, Dr. Bilyaminu ya ce:

“Za mu tattauna yadda ƙa’idojin Musulunci za su iya jagorantar kirkire-kirkire a harkar kuɗin dijital, domin tabbatar da gaskiya, haɗin kai, da rabon alheri ga kowa.”
“Taken taron na wannan shekara yana nuna jajircewarmu wajen gina tsarin tattalin arziki na gaskiya da ɗabi’a wanda zai amfani kowa da kowa.”
Sheikh Pantami da Bala Lau.
Hoton Farfesa Isa Ali Pantami da na shugaban Izala, Sheikh Bala Lau Hoto: Prof. Isa Ali Pantami, Jibwis Nigeria
Source: Facebook

Pantami ya fadi amfanin fasahar AI

A wani rahoton, kun ji cewa Farfesa Isa Ali Pantami ya kwantar da hankulan masu fargabar cewa mutane za su iya ra ayyuka saboda zuwa fasahar AI.

Kara karanta wannan

Magana ta kare, Tinubu ya rantsar da sabon shugaban hukumar zaben Najeriya

Pantami, wanda babban malamin addinin Musulunci ne ya ce maimakon haka fasaha za ta samar da sababbin damarmakin aiki ga waɗanda suka kware a harkar.

Tsohon ministan ya jaddada cewa AI na taka muhimmiyar rawa a ci gaban ilimi da tattalin arziki, yana mai cewa babu wata ƙasa da za ta cigaba idan ta yi watsi da wannan sabuwar fasaha.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262