Fitattun 'yan Najeriya 5 da ke jan ragamar shugabancin wasu manyan hukumomin duniya

Fitattun 'yan Najeriya 5 da ke jan ragamar shugabancin wasu manyan hukumomin duniya

Najeriya kasa ce da ke da albarkatun kasa masu dimbin yawa baya ga hakan Allah ya albarkaci kasar da mutane da ke yin ayyuka da dama a fadin duniya.

Fitattun 'yan Najeriya 5 da ke jan ragamar shugabancin wasu manyan hukumomin duniya
'Yan Najeriya 5 da ke jan ragamar shugabancin wasu manyan hukumomin duniya. Hoto: Daily Trust/The Nation
Asali: Facebook

A wannan rahoton, The Nation ta kawo jerin wasu 'yan Nigeria da ke jagorantar wasu hukumomi na duniya wanda hakan yasa 'yan Nigeria na alfahari da su.

1. Amina Jane Mohammed

Fitattun 'yan Najeriya 5 da ke jan ragamar shugabancin wasu manyan hukumomin duniya
Mataimakiyar sakatariyar majalisar dinkin duniya, Amina J Mohammed. Hoto: UN
Asali: Depositphotos

An haife ta ne a kasar Birtaniya, mahaifinta Hausa/Fulani ne yayin da mahaifiyarta ma'aikaciyar jinya ne a Burtaniya.

Ta rike mukamin ministan muhalli a karkashin gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari daga 2015 zuwa 2017.

Kara karanta wannan

Da dumi-dumi: Hawaye sun kwaranya yayin da Najeriya ta sake rashi na wani tsohon sanata

A Janairun 2017, babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Antoni Guterres ya sanar da niyyarsa na nada Mohammed a matsayin mataimakiyar babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya.

Tun lokacin ta cigaba da yin ayyukanta yadda ya dace tare da bai wa kowa sha'awa.

2. Ngozi Okonjo-Iweala

Fitattun 'yan Najeriya 5 da ke jan ragamar shugabancin wasu manyan hukumomin duniya
Ngozi Okonjo-Iweala, shugaban WTO. Hoto: The Nation
Asali: Depositphotos

Ngozi Okonjo-Iweala ce mace ta farko kuma 'yar Afirka da aka nada a matsayin shugaban kungiyar kasuwanci ta duniya, WTO.

Mrs Okonjo-Iweala ta yi aiki a matsayin Ministan Kudi a karkashin shugabannin kasa Obasanjo da Goodluck Jonathan.

Kazalika, tana rike da mukami da kwamitin direktoci a kamfanoni fiye 500 a kungiyoyin babban bankin duniya.

3. Akinwumi “Akin” Adesina

Fitattun 'yan Najeriya 5 da ke jan ragamar shugabancin wasu manyan hukumomin duniya
Akinwumi “Akin” Adesina, shugaban bankin cigaban Afirka. Hoto: The Cable
Asali: UGC

Akinwumi tsohon Ministan Aikin Noma ne karkashin tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan.

Ya yi karatun digirinsa na farko a bangaren tattalin arzikin aikin noma daga jami'ar OAU.

An zabe shi a matsayin shugaban bankin cigaban nahiyar Afirka a 2015, an sake zabensa a karo na biyu a 2020.

Kara karanta wannan

An bankado yadda Buhari da Ministansa suka saba doka wajen bada kwangilar biliyoyi

Shine dan Nigeria na farko da ya fara rike mukamin.

4. Dr. Chikwe Ihekweazu

Fitattun 'yan Najeriya 5 da ke jan ragamar shugabancin wasu manyan hukumomin duniya
Dr. Chikwe Ihekweazu, tsohon shugaban NCDC. Hoto: The Nation
Asali: UGC

An nada tsohon shugaban cibiyar dakile cutattuka masu yaduwa, NCDC, Dr. Chikwe Ihekweazu a matsayin mataimakin DG na tattara bayannai na lafiya a Kungiyar Lafiya ta Duniya, WHO.

Nadin ya zo ne bayan irin jagoranci na gari da ya yi a Nigeria yayin bullar annobar coronavirus.

Ya samu horaswa a matsayin mai bincike ga cutattuka masu yaduwa kuma ya shafe kimanin shekaru fiye da 20 yana aiki a matakai da dama a hukumomin lafiya.

5. HE Mohammad Sanusi Barkindo

Fitattun 'yan Najeriya 5 da ke jan ragamar shugabancin wasu manyan hukumomin duniya
Mohammad Sanusi Barkindo, babban sakataren OPEC. Hoto: The Punch
Asali: Twitter

Muhammad Sanusi shine babban sakataren kungiyar kasashe masu albarkatun man fetur, OPEC.

Asalinsa mutumin Yola ne daga jihar Adamawa. Ya yi karatun digiri a harkar kimiyyar siyasa daga Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria.

Ya rike mukamai da dama a hukumomin gwamnatin jihohi da tarayya ciki har da NNPC kafin a nada shi mukamin a OPEC.

Kara karanta wannan

Yadda Tarayyar Turai ta kashe £130m wajen tallafawa 'yan gudun hijira a Borno

An fitar da jerin Musulmi 500 mafi ƙarfin faɗa aji a duniya, Buhari, Ɗangote, Ɗahiru Bauchi da Zakzaky na ciki

A baya, kun ji cewa Shugaban Nigeria Muhammadu Buhari yana cikin jerin musulmin duniya 500 mafi karfin fada aji kamar yadda cibiyar nazarin addinin Islama da ke Amman a Jordan ta fitar.

A kowane shekara cibiyar tana fitar da sabbin sunayen musulmi 500 mafi karfin fada aji a duniya.

Shugaba Buhari ne mutum na 16 a cikin jerin sunayen musulmi 500 mafi karfin fada aji a duniya a bana kamar yadda The Muslim 500 ta fitar.

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel