Sharif Lawal
6918 articles published since 17 Fab 2023
6918 articles published since 17 Fab 2023
Tsohon sanatan Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani, ya nuna cewa da wuya a iya samun shugaban da zai yi nasara idan Mai girma Bola Tinubu ya gaza a mulkin Najeriya.
Kungiyar dattawan jam'iyyar PDP na Arewacin Najeriya, sun caccaki ministan babban birnin tarayya Abuja. Sun zarge shi da yunkurin ruguza jam'iyyar PDP.
Jam'iyyar ADC mai adawa a Najeriya ta kori mataimakin shugabanta da wasu mutane a jihar Kaduna. Jam'iyyar ta zarge su da rashin da'a tare da cin dunduniyarta.
Jam'iyyar ADC mai adawa a Najeriya ta yi tsokaci kan ci gaba da tsare jagoran kungiyar IPOB, Nnamdi Kanu. Ta ce har yanzu lamarin yana gaban kotu.
Wasu mutane da ake zargin masu kwacen waya ne sun hallaka wata ma'aikaciyar lafiya a jihar Kaduna. Sun kashe ta ne yayin kokarin kwace wayar hannunta.
Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar III ya karyata zargin kisan Kiristoci a Najeriya. Ya bayyana cewa ko kadan babu kamshin gaskiya.
Kotun Koli ta shirya yanke hukunci kan karar da ke kalubalantar dokar ta bacin da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya a jihar Rivers har ta wata shida.
Jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya ta sake gamuwa da koma baya bayan dan majalisar wakilai daga jihar Benue, ya tattara kayansa ya koma jam'iyyar APC.
Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya bayyana cewa gwamnonin jam'iyyun adawa na yin tururuwa zuwa jam'iyyar APC ne saboda manufofin gwamnatin Tinubu.
Sharif Lawal
Samu kari