Abin da Tinubu Ya Gani, Ya Dauko Shettima a Matsayin Abokin Takaransa – Kungiya

Abin da Tinubu Ya Gani, Ya Dauko Shettima a Matsayin Abokin Takaransa – Kungiya

  • All Progressives Congress (APC) Rebirth Group tayi bayanin silar dauko Kashim Shettima a 2023
  • Aliyu Audu yace Sanata Kashim Shettima ya tabuka abin a yaba a lokacin da ya yi Gwamnan Borno
  • Audu shi ne shugaban kungiyar, ya yabi yadda Shettima da Babangana Zulum suka kawo cigaba

Abuja - Kungiyar All Progressives Congress (APC) Rebirth Group tayi bayanin abin da ya kawo Kashim Shettima ya samu takara a jam’yyar APC.

Vanguard ta rahoto shugaban kungiyar, Aliyu Audu yana cewa ayyukan da Sanata Kashim Shettima ya yi a Borno ya sa Bola Tinubu ya tafi da shi.

Alhaji Aliyu Audu yake cewa Kashim Shettima ya tabuka abin kirki a lokacin da ya yi gwamnan jihar Borno tsakanin Mayun shekarar 2011 da 2019.

A cewar shugaban kungiyar, Shettima ya yi kokari wajen hada-kan mutane mabanbantan addinai da kabilu yayin da ake rikicin Boko Haram.

Kara karanta wannan

Zaɓen Shugaban Ƙasa Na 2023: Jerin Buƙatun Da Shugabannin CAN Suka Gabatarwa Tinubu A Abuja

A wancan lokaci ‘yan ta’addan Boko Haram sun addabi yankin Arewa maso gabashin Najeriya. Kungiyar tace hakan bai hana Shettima yin aiki ba.

Audu ya yi wannan bayani a lokacin da sashen siyasa na Politics Hub na jaridar Vanguard ya tattauna da shugaban kungiyar magoya bayan.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bola Tinubu
Bola Tinubu da Kashim Shettima @officialasiwajubat
Asali: Facebook

A cewarsa, ‘dan takarar mataimakin shugaban kasar ya yi kokarin bunkasa bangaren kiwon lafiya da na ilmi alhali al’umma na cikin halin dar-dar.

Jawabin Aliyu Audu

“Kashim Shettima a bangare guda shi kadai ne Gwamnan da ya yi mulki a tsakiyar ta’addanci, ya iya hada-kan Borno duk da sabanin addini da kabilanci.
Ya bunkasa bangaren ilmi da kiwon lafiya a bangarori dabam-dabam da mutane ba su taba tunanin hakan zai yiwu a lokacin da ake tsakiyar ta’addanci ba.”

- Aliyu Audu

Jagoran na APC Rebirth Group yace Sanata Shettima ya kawo Farfesa Babagana Zulum wanda ya gaje shi a matsayin Gwamna lokacin da ya bar gadon mulki.

Kara karanta wannan

Dalilin Da Yasa Na Zabi Shettima Musulmi Dan Uwana, Tinubu Ya Yiwa CAN Bayani

An rahoto Aliyu Audu yana mai cewa duk jihohin da ke yankin Arewacin Najeriya babu jihar da ta samu cigaba kamar Borno a cikin shekaru 11 da suka wuce.

Tikitin Musulmi-Musulmi

A cewar Asiwaju Bola Tinubu, kun ji labari wadanda suke babatu saboda ya dauko Kashim Shettima, sun nemi su zama abokan takararsa a zabe mai zuwa.

Amma Tinubu bai kama sunan wadanda suka sa ran zama ‘yan takaran mataimakin shugaban kasa a APC ba, ya yi wannan bayani ne da ya zauna da CAN.

Asali: Legit.ng

Online view pixel