Da Ɗumi-Ɗumi: Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ASUU Ta Zaɓi Sabon Shugaba

Da Ɗumi-Ɗumi: Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ASUU Ta Zaɓi Sabon Shugaba

- Ƙungiyar malaman jami'o'i ta ƙasa ASUU ta bayyana sabbon shugaban ta bayan kammala wa'adin farfesa Ogunyemi

- Farfesa Emmanuel Osodeke, shine ƙungiyar ta zaɓa a matsayin sabon shugabanta, wanda shine mataimakin shugaba a baya

- Ƙungiyar ta gudanar da zaɓen ne a yayin wani taron kwana uku da tayi a jami'ar Nnamdi Azikiwe dake jihar Anambra

An bayyana mataimakin shugaban ƙungiyar ASUU, Emmanuel Osodeke, a matsayin Sabon shugaban ƙungiyar bayan kammala wa'adin farfesa Biodun Ogunyemi a satin daya gabata, kamar yadda vanguard ta ruwaito.

KARANTA ANAN: Da Ɗumi-Ɗumi: Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisa a Jihar Nasarawa

An zaɓi Mr Osodeke, Farfesa a ɓangaren kimiyyar ƙasa a jami'ar koyon aikin gona, jihar Abia, ranar Lahadi a wajen taron ƙungiyar da ya gudana a jami'ar Nnamdi Azikiwe Awka, jihar Anambra.

Sabon shugaban zai amsa daga hannun Farfesa Biodun Ogunyemi na jami'ar Olabisi Onabanjo dake jihar Ogun, kamar yadda Premium times ta ruwaito.

Da Ɗumi-Ɗumi: Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ASUU Ta Zaɓi Sabon Shugaba
Da Ɗumi-Ɗumi: Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ASUU Ta Zaɓi Sabon Shugaba Hoto: vanguardngr.com
Asali: UGC

Sauran waɗanda aka zaɓa ɗin sun haɗa da: Chris Piwuna daga jami'ar Jos, a matsayin mataimakin shugaba; Olusiji Sowande daga jami'ar koyon aikin gona (FUNAAB), Abekuta, a matsayin ma'ajiyin kudi.

Farfesa Ade Adejumo, daga jami'ar Ladoke Akintola (LUTECH), Ogbomoso, a matsayin sakataren kuɗi;Austen Sado daga jami'ar Patakwal a matsayin sakataren Zuba jari.

KARANTA ANAN: Da Ɗumi-Ɗumi: Gwamna Ya Hana Amfani da Babur, Keke Nafef a Faɗin Jiharsa

Sauran sune: Adamu Babayo daga jami'ar Abubakar Tafawa Balewa(ATBU) Bauchi, a matsayin mai bincike, Stella-Maris daga jami'ar kimiyya da fasaha dake jihar Rivers, a matsayin sakataren walwala.

Tsohon shugaba, Mr Ogunyemi, zai cigaba da aiki tare da sabbin shugabannin da aka zaɓa domin taimaka musu wajen jagorancin ƙungiyar.

A wani labarin kuma Rundunar Yan Sanda Ta Damƙe Mutum Huɗu Ɗauke da Makamai a Jihar Kogi

Rundunar yan sanda reshen jihar Kogi ta bayyana cewa ta damƙe wasu mutum huɗu ɗauke da makamai a jihar.

Kakakin hukumar na juhar, William Aya, yace jami'an Operation Puff Ander ne suka kama waɗanda ake zargin.

Asali: Legit.ng

Online view pixel