AFCON: Cikakken Sunayen ’Yan Wasan Najeriya 5 da Suka Fi Zura Kwallaye a Tarihin Gasar

AFCON: Cikakken Sunayen ’Yan Wasan Najeriya 5 da Suka Fi Zura Kwallaye a Tarihin Gasar

Tawagar kungiyar kwallon kafa ta Najeriya, Super Eagles ta samu tsallakawa zuwa zagayen kusa da na karshe wato sami fainal bayan doke kasar Angola.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Najeriya ta yi nasara kan kasar Angola da ci daya mai ban haushi a ranar Juma’a 2 ga watan Faburairu.

'Yan wasa 5 da suka fi zuwa kwallaye a gasar AFCON a Najeriya
Sunayen ’Yan Wasan Najeriya 5 da Suka Fi Zura Kwallaye. Hoto: Ben Radford/KHALED DESOUKI/AFP/Henri Szwarc/Bongarts.
Asali: Getty Images

Jerin 'yan wasan 5 a Najeriya

Wannan shi ne karo na 16 da kasar ta samu damar zuwa matakin sami fainal bayan nasarori a sauran wasannin baya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Legit Hausa ta jero muku ‘yan wasa biyar da suka fi kowa shan kwallaye a gasar AFCON ga Najeriya.

Kara karanta wannan

Mark Zuckerberg ya zarce Bill Gates a arziki, Dangote ya samu ribar dala biliyan 1 a mako 1

1. Rashidi Yekini

Marigayi Rashidi Yekini shi ne ya fi kowa shan kwallaye ga kasar Najeriya inda ya jefa kwallaye 13 a gasar.

Yekini har ila yau, shi ne dan wasan da yafi kowa shan kwallaye a kasar baki daya da kwallaye 37.

2. Austin Jay-Jay Okocha

Okocha shi ne na biyu bayan ya sha kwallaye bakwai a gasar AFCON inda ya fara shan kwallo a 2000, cewar Soccernet.

Okocha ya zama dan wasan da ya fi kowa bajinta a gasar Tunisia 2004 tare da shan kwallaye hudu a gasar.

3. Segun Odegbami

Segun shi ne dan wasa na uku da yafi kowa shan kwallaye a kasar da kwallaye shida.

A wasansa na farko ya sha kwallaye uku a shekarar 1978 a gasar da aka gudanar a kasar Ghana.

4. Julius Aghahowa

Aghahowa shi ma ya sha kwallaye har guda shida a gasar AFCON da ya buga a rayuwarsa.

Kara karanta wannan

AFCON 2023: Hanyoyi 3 da tawagar Najeriya za ta iya doke Afrika ta Kudu a wasan kusa da na karshe

5. Odion Ighalo

Ighalo shi mutum na biyar a jerin wadanda suka fi kowa shan kwallaye a gasar AFCON, cewar The Nation.

Dan wasan ya sha kwallaye biyar inda ya zama wanda ya fi kowa shan kwallaye a gasar da aka yi a Masar a shekarar 2019.

Osimhen ya ji rauni a gasar AFCON

Kun ji cewa akwai hasashen cewa zai yi wahala Victor Osimhen ya buga wasa da kasar Afirka ta Kudu.

Daga bisani likitoci sun yi kwakkwaran bincike inda suka tabbatar Osimhen zai iya buga wasan su da kasar Afirka ta Kudu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel