Albashin ma'aikata
Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu ya amince da karin N35,000 a albashin ma'aikatan gwamnatin jihar, da alawus na kashi 50% na albashin Disamba.
Kana bukatar aikin taimakawa da aikace-aikace a ofishin jakadancin Amurka da ke Lagas Najeriya. Duba albashin da za a biya da ranar rufe neman aikin.
IPPIS ya jawo albashin ma’aikata fiye da 600 ya tsaya, ba za a cigaba da biyansu ba. Ma'aikatan ba su halarci tantancewar da aka yi domin gano ma'aikatan karya ba.
Ƙungiyar yan kasuwa (TUC) ta bukaci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta biyan dukkanin ma'aikantan gwamnatin tarayya karin albashin N35,000.
Gwamnatin Tarayya ta dakatar da biyan kudaden rage radadin cire tallafi na ma'aikata dubu 35 da aka fara a watan Satumba, kungiyar NLC ta yi barazanar yajin aiki.
Shahararriyar ma'aikaciyar gidan talabijin na NTA, Aisha Bello ta riga mu gidan gaskiya a jiya Lahadi 10 ga watan Disamba, an bayyana lokacin jana'izarta.
Gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris, ya amince da biyan kudin gratuti ga ma'aikatan da suka yi ritaya ko suka rasu a matakin jiha da kananan hukukomi a jihar.
Tsohon gwamnan jihar Edo kuma tsohon shugaban kungiyar kwadago ta kasa (NLC), Adams Oshiomole, ya bukaci NLC ta tabbatar an biya ma'aikata karin albashin N35,000.
Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki, ya shirya gwangwaje ma'aikatan jiharsa a yayin da shekarar nan ta 2023 ta kawo karshe. Gwamnan zai biya albashin watan 13.
Albashin ma'aikata
Samu kari