Aikin noma a Najeriya
Gwamna Abba Yusuf na Kano ya amince da fitar da Naira biliyan 5.07 domin sayo taki wanda za a rabawa manoma matsayin tallafi a kokarin bunƙasa harkar noma a jihar.
Hedikwatar tsaro ta kwantar wa da manoman kasar nan hankali, inda ta ce ta yiwa ayyukanta garanbawul yadda zai ba ta damar tsare rayukansu idan za su je gona.
Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya jaddada kudirinsa na ganin cewa an samu wadataccen abinci a Najeriya wanda hakan zai rage talauci da bunkasa tattalin arziki.
Hukumar kididdiga ta kasa ta bayyana jihohin da farashin kayan abinci ya fi kamari a lokacin da 'yan Najeriya ke fafutukar neman kudin da za su ciyar da kansu.
Manoma a Dansoshiya da ke karamar hukumar Kiru a Kano sun shiga zaullumin yadda su ke zargin kwamishinan ma'aikatar noma da kokarin kwace gonakinsu.
Gwamnatin jihar Borno ta samar da taki tirela 100 ga manona a jihar, za a sayar da takin ne kan saukin kashi 50%. Umar Usman Kadafur ne ya kaddamar da shirin.
Manoma a kauyen Unguwar Jibo da na Nasarawa-Azzara da ke a karamar hukumar Kachia, jihar Kaduna sun biya 'yan bindiga N6.2m domin a barsu su yi noma.
Gwamnatin Gombe za ta kashe naira biliyan 20 kan gina titi mai tsawon kilomita 18.5 a ciki da wajen kwaryar jihar. Kwamishinan ayyuka na jihar ne ya sanar da haka.
Karamin ministan noma da samar da abinci, Sanata Aliyu Abdullahi ya ce gwamnatin tarayya na kashe dala biliyan 1.5 duk shekara domin shigo da madara daga waje.
Aikin noma a Najeriya
Samu kari