Siyasar Najeriya
Kungiyar Matasa Arewa ta zargi Amaechi, Bafarawa da Shinkafi da yunkurin tayar da zaune tsaye ga gwamnatin Tinubu. Ta nemi jami'an tsaro su dauki matakin gaggawa.
Hukumar zaɓe ta kasa mai zaman kanta watau INEC ta ce babu buƙatar sai ta gabatar da waya shaida kan sakamakon zaben gwamnan jihar Edo da aka yi a 2024.
Hadimin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, Daniel Bwala, ya caccaki tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai. Ya ce Tinubu bai damu da kalamansa ba.
Sanata Ned Nwoko wanda ya sauya sheƙa zuwa APC ya fara cika baki, ya gargaɗi gwamnan jiharsa ta Delta da ya yi zamansa a PDP kar ya yi gigin sauya sheƙa.
Shugaban APC na kasa Abdullahi Umar Ganduje ya ce sun shirya kwato jihar Delta daga hannun PDP a zabe mai zuwa. Ya fadi haka ne yayin karbar Sanata Nwoko
Sanata Barau Jibrin da Bamidele sun maida martani ga Abba Moro yayin da ya yi ikirarin cewa sauya sheƙar Sanata Ned Nwoko ta saɓa wa doka saboda PDP ba rabe ba.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar ya ziyarci tsohuwar ƴar takarar gwamnan Adamawa a inuwar APC, Sanata Aishatu Binani a gidanta da ke Abuja.
Majalisar amintattun PDP ta ƙasa watau BoT ta kira taron gaggawa a babban birnin tarayya Abuja domin tattauna halin da jam'iyyar ta tsinci kanta a ciki.
Jam'iyyar NNPP ta zaɓi Agbo Major a matsayin sabon shugaban jam'iyyar na ƙasa a taron da aka gudanat ranar Talata zuwa Laraba, an zaɓi wasu shugabanni.
Siyasar Najeriya
Samu kari