Siyasar Najeriya
An fara samun matsala a haɗakar yan adawa bayan Kungiyar “Concerned Stakeholders of the ADC” ta bayyana damuwa kan nadin sababbin shugabannin a ADC.
Shugabanni gunduma a jihar Nasarawa sun yanke shawarar dakatar da shugaban APC na jiha, Hon. Aliyu Bello bisa zarginsa da ayyukan cin amana da zagon ƙasa.
Aregbesola ya sauya akida daga na hanun daman Tinubu zuwa sakataren ADC, bayan lalacewar dangantakarsu, yana mai alƙawarin gina jam'iyyar gabanin zaɓen 2027.
Peter Obi ya mika bukatar yin takara wa'adi daya ga gamayyar 'yan adawa a Najeriya. Obi ya ce zai yi takara sau daya ba tare da yin tazarce ba a 2031.
Hukumar zabe ta INEC ba shirin kawo sauye sauye game da yadda ake duba sakamakon zabe da aka riga aka fitar. INEC za ta shirya zabe a jihohi a wata 13 masu zuwa.
An hana su Atiku dakin taron kaddamar da ADC a Abuja ba zato ba tsammani. 'Yan adawar sun ce ba za su ja da baya ba yayin da suka zargi sa hannun gwamnati.
Yayin da shirin kwace mulki daga hannun APC ke ƙara kankama, tsohon shugaban Majalisar Dattawa, David Mark ya fice daga jam'iyyar PDP a jihar Benue.
Ƙungiyar adawa ta Atiku ta zaɓi ADC don doke Tinubu a 2027, tare da naɗa David Mark da wasu ƙwararru a matsayin shugabanni, yayin da take kuma neman rajistar ADA.
Jam'iyyar APC ta ce 'yan adawa masu kokarin hada kai a ADC ba za su yi tasiri a kan Bola Tinubu ba. Mai magana da yawun APC ya ce su za su yi nasara a 2027.
Siyasar Najeriya
Samu kari