Labaran garkuwa da mutane
Sanata Shehu Sani na kan ra'ayin cewa, bata lokaci ne gwamnati ta tsaya wani tattaunawa da 'yan bindigan da suka addabi jama'ar gari. Ya bayyana dalilinsa uku.
Yan bindiga sun kashe Faston RCCG tare da yin garkuwa da mutane 7 yayin da ake tsaka da bauta a cocin Abule-Ori, karamar hukumar Obafemi Owode ta jihar Ogun.
Mataimakin shugaban kungiyar makiyayan Najeriya ta Miyyeti Allah (MACBAN) na kasa, Injiniya Munnir Atiku Lamido ya bata. Munnir na a hanyarsa ta zuwa Kaduna ne.
Masu garkuwa da mutane sun sako amarya mai suna Rukkayat Musa da ƙannen mijinta mata guda biyu da suka sace a jihar Kwara. An biya N7m a matsayin kuɗin fansa.
DSS ta ankarar da al’umma cewa akwai shirye-shirye aukawa wuraren bauta da filayen wasanni. Dr. Peter Afunanya ya ce DSS da Sojoji da ‘Yan Sanda sun gano hakan.
Wasu tsagerun 'yan bindigan daji sun sheƙe manoma uku, sun tattara wasu manoman da matafiya da ke kan hanyar zuwa kasuwa a Birnin Gwari da ke jihar Kaduna.
'Yan bindiga sun sace wata manajar bankin Sterling Mai suna Nneka Unoka a jihar Bayelsa yayin da take kan hanyarta na zuwa wurin aiki a cikin birnin Yenagoa.
Yan bindiga sun yi garkuwa da basarake Shedrack Durojaiye Obibeni, da mai ɗakinsa a ƙaramar hukumar Yagba ta Gabas da ke jihar Kogi, da yammacin ranar Litinin.
Wasu yan bindiga da ba'a san ko su waye ba sun halaka ma'aikacin hukumar zabe INEC, Emmanuel Igwe, a jihar Ebonyi yayin da yake hanyar dawowa daga jihar Abiya.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari