Zaben Najeriya
A halin yanzu an kawo karshen zaben gwamna a rumfunan zabe da dama a jihar Kogi kuma tuni jami'an Hukumar Zabe mai Zaman Kanta (INEC) sun fara kidaya kuri'u.
Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma ya lashe dukkanin ƙananan hukumomi 27 a zaɓen gwamnan jihar Imo da aka gudanar a ranar Asabar, 11 ga watan Nuwamban 2023
Ƴan takarar gwamnan jam'iyyun PDP da LP a jihar Imo, sun nemi da a soke zaɓen gwamnan jihar na ranar Asabar, 11 ga watan Nuwamba, saboda maguɗin zaɓe.
Wakilin jam'iyyar Labour Party (LP) a cibiyar tattara sakamakon zaɓen gwamnan jihar Imo, ya sha dukan tsiya ana tsaka da tattara sakamakon zaɓen.
Dele Momodu hadimin Atiku Abubakar, ya caccaki hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) kan dakatar da zaɓe a wasu gundumomi tara a jihar Kogi.
Wani ma’aikacin hukumar INEC da aka yi ram da shi a ranar jaji-birin zaben Gwamnonin jihohi, ya samu ‘yanci. Sanarwa ta fito daga INEC cewa malamin zaben ya tsira.
Jami’an Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) sun kama wasu mutane 14 da ake zargi da sayen kuri’u a rumfunan zabe a Bayelsa da Imo.
Yanzu nan labari ya zo cewa Hukumar INEC ta bada sanarwar dakatar da zaben sabon gwamna a wasu daga cikin bangarorin jihar Kogi kamar yadda wasu su ke kira.
Al'umma suna nan sunyi zugum suna jiran ganin yadda za ta kaya a yayin da hukumar zabe INEC ke shirin gudanar da zabukan gwamba a jihohin Kogi, Bayelsa da Imo.
Zaben Najeriya
Samu kari