Zaben Najeriya
Rotimi Amaechi ya ce Najeriya ta lalace, inda ya zargi INEC da jam'iyyar APC (da ya ce 'ya'yanta barayi ne) da shirya murɗe zaɓuka masu zuwa. Ya koma ADC.
Yayin da ake taron hadaka a Abuja, tsohon Ministan Shari'a, Abubakar Malami ya fice daga jam’iyyar APC tare da shiga ADC, yana cewa Najeriya na cikin mawuyacin hali.
An fara samun matsala a haɗakar yan adawa bayan Kungiyar “Concerned Stakeholders of the ADC” ta bayyana damuwa kan nadin sababbin shugabannin a ADC.
An yi ta yada rade-radin cewa Bola Ahmed Tinubu zai sauya Kashim Shettima a matsayin mataimaki a zaben 2027 da ke tafe a nan gaba wanda fadar shugaban ta karyata.
Aregbesola ya sauya akida daga na hanun daman Tinubu zuwa sakataren ADC, bayan lalacewar dangantakarsu, yana mai alƙawarin gina jam'iyyar gabanin zaɓen 2027.
A labarin nan, za a ji cewa har yanzu ana samun manyan yan siyasa da ake ganin za su maye gurbin Dr. Abdullahi Umar Ganduje bayan da ya yi murabus.
Hukumar zabe ta INEC ba shirin kawo sauye sauye game da yadda ake duba sakamakon zabe da aka riga aka fitar. INEC za ta shirya zabe a jihohi a wata 13 masu zuwa.
A labarin nan, za a ji cewa hadakar yan adawa ta shirya sanar da jam'iyyar ADC a matsayin wacce za a hadu a cikinta domin korar Bola Tinubu daga ofis.
Jagoran jam'iyyar LP a Najeriya, Peter Obi ya jaddada aniyarsa ta yin takarar shugaban kasa a zaben 2027. Ya ce zai yi wa'adi daya kawai idan ya samu nasara.
Zaben Najeriya
Samu kari