Atiku Abubakar
Hadimin shugaban kasa, Daniel Bwala ya shawarci Atiku Abubakar ya haƙura da neman zama shugaban kasa domin babu alamar Allah zai ba shi damar shugabanci.
Tsohon sakataren gwamnati, Babachir Lawal ya ce Shugaba Bola Tinubu na cikin ruɗani saboda haɗakar adawa da Atiku Abubakar da Nasir El-Rufai ke jagoranta.
Gwamnonin jihohin da APC ke mulki sun karyata jita jitar da aka yada cewa za su juya baya ga Bola Tinubu a zaben 2027. An yi zargin cewa za su hade da Atiku.
Hakeem Baba-Ahmed ya bukaci Atiku Abubakar da Shugaba Tinubu da su hakura da takara a 2027, su ba matasa dama su kawo sababbin dabaru don kawo babban ci gaba a kasa.
Wata majiya ta ce Atiku Abubakar da Peter Obi na shirin hada kai domin kawar da gwamnatin Bola Tinubu a zaben 2027, bayan sun gane cewa hadin guiwa ce mafita.
Wasu daga cikin manyan abokan tafiyar siyasar Atiku Abubakar sun fara juya masa baya tun kafin zaben 2023, kuma an ci gaba da samun masu barin PDP.
Hadimin ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, Lere Olayinka, ya bayyana cewa hadakar da Alhaji Atiku Abubakar ke jagoranta ta mutu murus.
Ministan Abuja, Nyesom Wike ya zargi Dele Momodu da mara wa Atiku Abubakar saboda kudi, tare da zargin cewa tsohon dan takarar ne ya jawo masu matsala.
Shugabannin kungiyar daliban Arewacin Najeriya a jihohi 19 sun ziyarci Atiku Abubakar a gidansa da ke Abuja. Atiku ya ce zai yi aiki tare da matasa wajen gina kasa.
Atiku Abubakar
Samu kari