Arewa
An sanar da rasuwar yadikkon Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi, Hauwa Duguri ta rasu a ranar 1 ga Janairu 2025 tana da shekaru 120 da haihuwa.
Sojojin Najeriya sun kashe wasu manya manyan shugabannin ‘yan bindiga da suka hada da Halilu Sububu a karkashin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu a shekarar 2024.
Zainab Ado-Bayero ta yi barazanar kawo karshen rayuwarta sakamakon wahalar rayuwa da rashin tallafi tun bayan rasuwar mahaifinta, tsohon sarkin Kano.
Rahotanni sun tabbatar da cewa wasu ‘yan bindiga sun sace shugaban ƙungiyar KUDA, Emmanuel Tor Yaji, a Tsar Mbaduku, yankin ƙaramar hukumar Vandeikya, jihar Benue.
Sanata Shehu Sani ya ziyarci makabartar tarihi da aka birne sarakunan Arewa da suka yaki turawan mulkin mallaka a Lokoja. Sanatan ya bukaci a karrama sarakunan.
Sanusi II ya bukaci kasashen Yamma su zuba jari a Arewa ta hanyar gina makarantu, asibitoci da masana’antu, maimakon yin wa'azin da zai jawo kiyayya tsakanin addinai
Yayin da ‘yan arewa ke adawa da batun haraji, Jide Ojo ya shawarci Tinubu da ka da ya janye kudurin. Ya kuma yi bayani kan goyon bayan da Tinubu zai samu a 2027.
Shugaba Bola Tinubu ya amince a kafa jami'ar tarayya a Kudancin Kaduna domin ci gaban ilimi. Mataimakin Shugaban kasa, Kashim Shettima, ya bayyana hakan.
An ruwaito cewa, gwamnatin Najeriya ta kashe makudan kudade domin tabbatar da an shiryar da 'yan Boko Haram tare da maida su mutane kamar kowa a kasar.
Arewa
Samu kari