Arewa
Jimami yayin da mawaki Dauda Abdullahi Kahutu Rarara ya yi hatsarin mota a kan hanyarsa ta zuwa filin tashi da saukar jiragen sama a yau Juma'a 22 ga watan Satumba.
Wasu 'yan bindiga sun kai farmaki a Jami'ar Gwamnatin Tarayya a Gusau tare da sace dalibai a dakunansu na kwana har guda uku a daren jiya da misalin 3 na dare.
Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Musa Ibrahim Faskari ya shawarci mutane da su dauki makamai don kare kansu daga hare-haren 'yan bindiga a Najeriya.
Rundunar 'yan sanda a jihar Kano ta dage dokar hana fita da ta kafa a jihar a jiya Laraba 20 ga watan Satumba bayan yanke hukuncin kotun sauraran kararrakin zabe.
Shugaban jam'iyyar APC a jihar Kano, Abdullahi Abbas ya jagoranci murnan cin nasarar jam'iyyar a kotun zaben gwamnan jihar da ta bai wa Nasiru Gawuna nasara a yau.
An shiga wani irin yanayi a jihar Kano bayan yanke hukuncin kotu da ta kwace kujerar Gwamna Abba Kabir inda ta tabbatar da Nasiru Gawuna na APC a matsayin gwamna.
Kungiyar Dattawan Arewa, NEF ta yabawa Shugaba Tinubu kan nadin kakakinta, Dakta Hakeem Baba-Ahmed matsayin hadimin mataimakinsa, Kashim Shettima.
Kotun sauraran kararrakin zabe a jihar Gombe ta rusa nasarar zaben kakakin majalisar jihar, Abubakar Luggerewo inda ta bai wa jam'iyyar PDP nasara.
Gwamnatin jihar Katsina ta amince da tube Sarkin Kuraye, Alhaji Abubakar Abdullah kan daura aure ba bisa ka'ida ba wanda daya daga cikinsu ke dauke da cuta.
Arewa
Samu kari