Arewa
'Yan bindiga sun yi ajalin mutane 24 wadanda mafi yawansu 'yan banga ne a karamar hukumar Sabuwa da ke jihar Katsina a daren ranar Alhamis 2 ga watan Mayu.
Hukumar EFCC ta na zargin akalla tsofaffin gwamnoni 54 a Najeriya da badakalar N2.187trn yayin da suke mulkin jihohinsu daban-daban tun bayan dawowar dimukradiyya.
Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya kare matakin gwamnonin Arewa na zuwa kasar Amurka taro kan matsalar rashin tsaron da ta addabi yankin.
Wasu hatsabiban 'yan bindiga sun sake kai mummunan hari a karamar hukumar Birnin Gwari a Kaduna inda suka sace Dagatai biyu da hallaka 'yan banga takwas.
Tsohon gwamnan jihar Katsina, Barista Ibrahim Shema ya watsar da jami'yyar PDP mai adawa inda ya sauya sheka zuwa APC mai mulkin jihar a yau Alhamis.
Wata daliba daga Arewacin Najeriya, Fatima Saleh Alkali ta burge mutanan kasar bayan samun maki 336 a jarrabawar UTME da aka gudanar a kwanakin baya.
Yayin da ake bikin ranar ma'aikata a Najeriya, jami'yyar PDP ta bukaci a binciki Nasir El-Rufai kan korar ma'aikata 27,000 ba tare da biyansu hakkokinsu ba.
Shugaban kungiyar NGF, Gwamna Muhammadu Yahaya na jihar Gombe, ya koka kan cewa a Arewacin Najeriya ce lamba 1 a yawan yaran da basu zuwa makaranta a duniya.
A Nahiyar Afirka akwai kasashe da dama da ke da masu amfani da harshen Hausa wandanda suka yi tashe dalilin harkokin kasuwanci da kuma sana'o'i da suka kware.
Arewa
Samu kari