Yan ta'adda
An kashe jami’an tsaro 326 a Najeriya cikin shekara guda. Ƴan sanda 258, sojoji 59 sun mutu yayin da su ma NSCDC da hukumar shige da fice suka rasa jami’ansu.
ACP Dauda Fika, jarumin dan sanda da ke yaki da Boko Haram, ya rasu a Abuja. Ya jagoranci hare-haren kwato garuruwa a Yobe da Borno daga hannun ‘yan ta’adda.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasara kan 'yan ta'adda a jihar Borno. Dakarun sojojin sun hallaka 'yan ta'adda tare da kwato makamai masu yawa.
Masu garkuwa sun kashe mutum ɗaya, sun sace huɗu a jihar Filato. Shugaban ƙaramar hukuma ya yi kira da a ceto su, ya kuma ziyarci yankin don tantance lamarin.
Kachallah Bammi Yarma ya dawo Katsina bayan shekaru tara a gidan yari a kasar Nijar. Bayyanarsa na iya ƙara tashin hankali a yankin Arewa maso Yamma.
Rundunar sojin Najeriya ta kama wani mai safarar makamai yayin da suke sintiri a Filato. An kama motar makamai yayin da sauran mutanen suka tsere.
'Yan sandan jihar Kano sun sanar da mutuwar wani gagararren dan daba bayan mutane sun masa dukan kawo wuka, sun yi rugu rugu da kafofinsa kafin ya mutu.
Sojojin Najeriya sun kai farmaki maboyar 'yan bindiga a jihar Taraba sun kama miyagu 23. 'Yan ta'addar sun biya wani basarake N1.5m domin kafa sansani.
An sake samun wani sabon bidiyo da ya nuna Kachallah Bugaje wanda ya koma Zakiru yana jagorantar addu’a tare da yaransa, bayan da ya ce ya daina ta’addanci.
Yan ta'adda
Samu kari