Zai Shiga APC ne? Sule Lamido Ya Shirya Ganawa da Shugaba Bola Tinubu
Bamaina, Jigawa – Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya bayyana cewa a shirye yake ya gana da Shugaba Bola Ahmed Tinubu idan aka gayyace shi, matukar hakan zai amfani hadin kai da cigaban Najeriya.
Sule Lamido, wanda yana daya daga cikin wadanda suka kafa jam'iyyar PDP a 1998, ya jaddada burinsa na warwrae duk wata matsala da ta addabi kasar nan don samun ci gaba.
Lamido ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da jaridar The Nation a garinsu Bamaina a ranar Sallah, inda ya ce ba shi da wata matsala wajen tattaunawa da shugaban kasa idan hakan zai taimaka wa kasa.
“A shirye nake fiye da kowa. To yaushe za mu tafi mu gan shi?” yana mai jaddada aniyarsa ta shiga tattaunawa mai amfani.
Lamiso ya musanta zargin shiga APC
Sai dai tsohon gwamnan ya musanta rade-radin da ke cewa ya ƙi karbar gayyatar shiga jam’iyyar APC mai mulki, yana mai cewa ba a taba yi masa irin wannan tayin ba.
“Yaushe aka gayyace ni? Don Allah ku fada min. Shin ya aiko ku ne? Ni yanzu ne na fara jin wannan maganar.”
Lamido ya jaddada cewa duk wata hulda tsakaninsa da shugaban kasa ya kamata ta kasance ne bisa muradun kasa, ba wai siyasa ta bangare ba.
Ya ce: “Idan maganar cigaba da bunkasar Najeriya ce, a shirye nake. Zan iya ganawa da shi.”
Asali: Legit.ng
