FG Ta Yi Martani Kan Kirayen Tinubu Ya Yi Murabus Domin Wahalar Rayuwa, Bayanai Sun Fito

FG Ta Yi Martani Kan Kirayen Tinubu Ya Yi Murabus Domin Wahalar Rayuwa, Bayanai Sun Fito

FCT, Abuja - Ministan yada laarai da wayar da kan kasa, Mohammed Idris, ya bada dalilin da yasa Shugaba Bola Tinubu ba zai yi murabus ba duk da tsadar rayuwa da ake fama da shi a Najeriya.

Ministan, wanda ya ke martani kan kiran da gwamnonin jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta yi kan cewa Shugaba Tinubu ya yi murabus idan ba zai iya magance wahalar rayuwa da ake fama da shi a kasar ba, ya ce PDP ta yi aikinta idan an zabe su.

Idris a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, 18 a watan Fabrairu ta hannun hadiminsa na musamman Rabiu Ibrahim, ya bayyana wannan kiran na cewa Tinubu ya yi murabus a matsayin wani mataki na kawar da hankalin mutane a maimakon mayar da hankali don tallafawa shugaban kasa ya kawo sauki ga 'yan Najeriya.

Kara karanta wannan

Rudani yayin da shahararriyar 'yar Tiktok, Murja Kunya, ta bar gidan yari

Wani sashi na sanarwar ministan ya ce:

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel