Gwamma Lawal Ya Kafa Tarihi, Ya Yi Abinda Ba a Taba Gani Ba Tunda Aka Kirkiro Jihar Zamfara
- Dauda Lawal ya kafa tarihin zama gwamna na farko da ya fara biyan ma'aikatan gwamnati albashi wata 13 a shekara ɗaya a Zamfara
- Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar a Gusau
- Ya ce ƙarawa ma'aikata albashin wata ɗaya ya nuna kudirin gwamna na inganta walwala da jin daɗin ma'aiktan gwamnati
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jihar Zamfara - Gwamna Dauda Lawal ya biya ma'aikatan gwamnati albashin watan 13 a jihar Zamfara, kamar yadda Channels tv ta ruwaito.
Gwamnatin jihar Zamfara ta sanar da yanke shawarar biyan ma'aikata albashi na watan 13 ranar Alhamis, 28 ga watan Disamba, 2023.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/80c1e7d00d9cc9b2.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Mutuwar Akeredolu: Shin Aiyedatiwa ne zai zama sabon gwamnan Ondo? Ga abin da doka ta ce
![Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara. Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara.](https://cdn.legit.ng/images/1120/819b89ca57474676.jpeg?v=1)
Asali: Facebook
Wannan mataki ne kunshe a wata sanarwa da shugaban hukumar kula da ma'aikatan jihar, Ahmed Aliyu Liman, ya fitar, cewar rahoton Tribune.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
An taba biyan albashin wata 13 a Zamfara?
A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamna, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ya bayyana cewa Dauda Lawal ya kafa tarihin da ba a taɓa yi ba a jihar Zamfara.
Kakakin gwamnan ya ce biyan ma'aikata albashin wata na 13 shi ne karo na farko da aka taɓa yi a tarihin jihar Zamfara da ke Arewa Maso Yamma.
A cewarsa, matakin ya yi daidai da kudurin gwamnatin jihar na kyautata jin dadi da walwalar ma’aikata da kuma zaburar da su yi kyakkyawan aiki yadda ya kamata.
Bala Idris ya ce:
"A yau ne Gwamna Dauda Lawal ya amince a gaggauta biyan alawus-alawus na karshen shekara ga ma’aikatan gwamnati a jihar Zamfara."
"Irin wannan karimcin ana yinsa ne da nufin kara wa ma’aikata kwarin gwiwa da kuma ba su tallafin kudi a lokacin hutu.
“Yana da kyau kowa ya san cewa wannan shi ne karo na farko a tarihin Zamfara da gwamnatin jihar ta fara biyan ma’aikata albashin watanni 13 cikin shekara ɗaya."
"Wannan matakin ya nuna muradin Gwamna Lawal na aiwatar da tsare-tsare da zasu inganta yanayin aiki, karin albashi, da samar da damarmaki ga ma’aikatan gwamnati."
PDP ya jaddada matsaya kan sauya sheƙar yan majalisa 26
A wani rahoton kuma Jam'iyyar PDP ta ce ba gudu ba ja da baya kan kujerun ƴan majalisa 26 da suka sauya sheka zuwa jam'iyyar APC a jihar Ribas.
Adeyemi Ajibade (SAN), bai bada shawara kan shari'a na PDP ya ce duk da Tinubu ya warware rikicin Ribas amma ƴan majalisar sun rasa kujerunsu.
Asali: Legit.ng