Gabannin 2023, Gwamna Inuwa Yahaya Ya Yi Alkawarin Gina Masallaci da Coci a Kauyen Todi

Gabannin 2023, Gwamna Inuwa Yahaya Ya Yi Alkawarin Gina Masallaci da Coci a Kauyen Todi

  • Gwamnan jihar Gombe ya jaddada cewar shine zai sake lashe zaben gwamnan jihar a 2023
  • A cewar Gwamna Inuwa Yahaya, abokan hamayyarsa na sauran jam'iyyun siyasa basa razana shi ko kadan
  • A halin da ake ciki, gwamnan na jam'iyyar All Progressives Congress ya dau alkawarin gina coci da masallaci a kauyen Todi

Gwamna Inuwa Yahaya ya nanata cewa shine zai sake lashe zaben gwamnan jihar Gombe a 2023.

Yahaya wanda shine dan takarar gwamna na jam'iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar ya jaddada cewa babu mai iya ja da shi a tseren. A cewarsa, abokan hamayyarsa ba barazana bane ga kudirinsa na son zarcewa.

Inuwa Yahaya
Gabannin 2023, Gwamna Inuwa Yahaya Ya Yi Alkawarin Gina Masallaci da Coci a Kauyen Todi Hoto: Inuwa Yahaya
Asali: Facebook

Za a ginawa al'umman Todi masallaci, coci da makaranta

Ya yi hasashen ne a wata hira da manema labarai bayan gangamin yakin neman zabensa a gudunma daban-daban na karamar hukumar Billiri da ke jihar, jaridar Leadership ta rahoto.

Kara karanta wannan

Gwamnan Arewa Ya Tona Asirin 'Yan Siyasar Dake Jin Haushin Shigo da Na'urar BVAS a Zaben 2023

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Da yake ci gaba da bayani a kauyen Todi, gwamnan ya yi alkawarin gina masallaci, coci a gudunmar bayan gabatar da bukatar hakan da mazauna yankin suka yi.

Ya kuma ce zai gina makaranta, hanya da gada a yankin Billiri ta arewa wanda ke fama da zaizayan kasa, jaridar Vanguard ta kuma rahoto.

Gwamna Inuwa Yahaya ya magantu a kan na'urar BVAS

A halin da ake ciki, Legit.ng ta rahoto a baya cewa Muhammad Inuwa Yahaya, ya ce ba ya tsoron matakin hukumar INEC ta dauka na amfani da na'urar tantance katunan zabe wato BVAS a zaben 2023.

Gwamnan na Gombe ya ce yan siyasan da basu da magoya baya sune suke fargabar sabon tsarin da hukumar zaben ta zo da shi.

Ya fadi hakan ne a wajen yakin neman zabensa wanda ya gudanar Garko, inda ya ce lallai talakawa na tare da shi har gobe.

Kara karanta wannan

Atiku Ya Sake Shiga Tasku, Gwamna Arewa Ya Ayyana Ɗan Takarar Da Zai Marawa Baya a 2023

A wani labari na daban, mun ji cewa yaran shugaban kasa Muhammadu Buhari, matamakinsa Yemi Osinbajo da Yusuf Bichi; shugaban hukumar DSS sun fito a jerin matasan da za su yiwa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu na APC kamfen gabannin zaben 2023.

Sunayen Zahra Buhari, Yusuf Buhari, Kiki Osinbajo da Abba Yusuf Bichi sun bayyana a jerin sunayen da jam’iyyar APC ta fitar a makon nan.

Asali: Legit.ng

Online view pixel