Gwamna Oyetola Ya Nada Sabbin Manyan Sakatarori 30 a Gwamnatinsa

Gwamna Oyetola Ya Nada Sabbin Manyan Sakatarori 30 a Gwamnatinsa

  • Gwamna Oyetola na jihar Osun ya zakulo mutane 30 daga ma'aikatan jiharsa ya naɗa su manyan Sakatarori
  • Shugaban ma'aikatan jihar, Festus Iyebade, ne ya sanar da haka ranar Alhamis, yace zasu cike guraben da ake da su a bangaren
  • Wannan na zuwa ne bayan gwamnan, mamban APC ya yi rashin nasara a zaben gwamnan da ya gabata a jihar a watan Yuli

Osun - Gwamnan jihar Osun, Adegboyega Oyetola, ya naɗa ma'aikata 30 a matsayin manyan Sakatarori a gwamnatinsa ranar Alhamis 24 ga watan Nuwamba, 2022.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa sunayen mutanen da gwamna Oyetola na jam'iyyar APC ya naɗa na ƙunshe ne a wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun shugaban ma'aikata, Dakta Festus Oyebade.

Gwamna Oyetola na jihar Osun.
Gwamna Oyetola Ya Nada Sabbin Manyan Sakatarori 30 a Gwamnatinsa Hoto: punchng
Asali: UGC

Sanarwan ta ƙara da cewa waɗanda Allah ya ci da aka naɗa su a matsayin manyan Sakatarorin zasu cike gurbin da ke akwai a sashin ma'aikatan gwamnatin jihar Osun, Daily Trust ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Jerin Talakawan Dake jihohin Gombe, Yobe, Taraba, Bauchi, Borno, Adamawa: NBS

Jerin sunayen waɗanda gwamnan ya naɗa

Legit.ng Hausa ta tattaro muku sunayen waɗanda wannan ci gaban ya shafa, sune kamar haka:

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

1. Injiniya Kamoru A. Babalola

2. Injiniya. S. O. Ajao

3. Mista M. A. K. Jimoh

4. Mista R. A. Popoola

5. Dakta D. O. Ogunrinade

6. Misi. J. K. Odediran

7. Mr. Oyesiku Adelu

8. Mista Babajide Falade

9. Misis Funmilola Oyewole

10. Mista O.A. Ogundun

11. Mista Bukola Aderibigbe

12. Mista Taiwo Oladunjoye

13. Dakta A. A Oni

14. Mista Lekan Babalola

15. Misis Sola Akinsola

16. Mista K.N. Akintola

17. Mista J. S. Adekomi

18. Misis Jibola Falode

19. Mis AY Esan

20. Misis C O Falade

21. Misis C O Fasina

22. Misis Gbemisola Fayoyin

23. Misis M. A Olawale

24. Mista S. A Raji

25. Kunle Adebayo

Kara karanta wannan

Waiwayen Tarihi: Lokuta 11 Da Aka Yi Wa Kudin Najeriya Sauye-Sauye Daga 1960

26. Mista T. O Akinwumi

27. Mista Richard Oyegbami

28. Mista Fatai Adekilekun

29. Mista M.O. Obidiya

30. Injiniya I. A Babalola.

Ku Yafe Mun Kura-Kuran da Na Tafka a Zamanin Mulkina, Masari Ya Roki Katsinawa

A wani labarin kuma kun ji cewa gwamna Masari na jihar Katsina ya roki al'umma su yafe masa idan ya yi kuskure a mulkinsa

Aminu Bello Masari, wanda zango na biyu na mulkinsa zai kare a watan Mayu, 2023, ya yi wannan roko ne a wurin kaddamar da kwamitin kamfe na Katsina.

Bugu da ƙari, gwamnan ya magana mai harshen damo inda yake cewa akwai wasu mutane duk abinda suka samu a gwamnatinsa ba su gode wa Allah ba.

Asali: Legit.ng

Online view pixel